< Nechemijas 8 >
1 Kad nu septītais mēnesis atnāca, un Israēla bērni bija savās pilsētās, tad visi ļaudis sapulcinājās kā viens vienīgs vīrs laukā priekš Ūdens vārtiem un sacīja uz Ezru, to rakstu mācītāju, lai tas atnes Mozus bauslības grāmatu, ko Tas Kungs Israēlim bija pavēlējis.
sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
2 Un priesteris Ezra atnesa bauslību draudzes priekšā, vīriem un sievām un visiem, kas to varēja saprast, pirmā dienā septītā mēnesī.
Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
3 Un lasīja no tās uz lauka Ūdens vārtu priekšā no pašas gaismas līdz pusdienai vīru un sievu priekšā, kas tik saprata, un visu ļaužu ausis (griezās) uz bauslības grāmatu.
Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
4 Un Ezra, tas rakstu mācītājs, stāvēja uz augsta koka krēsla, ko tie priekš tam bija uztaisījuši, un viņam sānis stāvēja Matatija un Šemus un Anaja un Ūrija un Hilķija un Maāseja viņam pa labo roku, un viņam pa kreiso roku Pedaja un Mišaēls un Malhija un Hašums un Hašbadanus, Zaharija, Mešulams.
Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
5 Un Ezra atdarīja to grāmatu priekš visu ļaužu acīm, jo viņš stāvēja augstāki nekā visi ļaudis, un kad viņš to atdarīja, tad visi ļaudis uzcēlās.
Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
6 Un Ezra teica To Kungu, to lielo Dievu, un visi ļaudis atbildēja: Āmen, Āmen! Savas rokas paceldami, un locījās un metās uz savu vaigu zemē priekš Tā Kunga.
Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
7 Un Ješuūs un Banus un Šerebija, Jamins, Akubs, Šabetajus, Hodija, Maāseja, Kelitus, Azarija, Jozabads, Hanans, Pelaja un tie leviti izskaidroja tiem ļaudīm bauslību, un tie ļaudis stāvēja savā vietā.
Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
8 Un tie lasīja no Dieva bauslības grāmatas tulkodami un izskaidrodami, ka lasot to varēja saprast.
Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
9 Tad Nehemija, tas ir tas zemes soģis, un priesteris Ezra, tas rakstu mācītājs, un tie leviti, kas tos ļaudis mācīja, sacīja uz visiem tiem ļaudīm: šī diena Tam Kungam, jūsu Dievam, ir svēta, neesiet noskumuši un neraudat. Jo visi ļaudis raudāja, kad tie dzirdēja bauslības vārdus.
Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
10 Tad viņš uz tiem sacīja: Ejat, ēdiet treknu un dzeriet saldu, un sūtiet daļas tam, kam nekā nav sataisīts. Jo šī diena mūsu Kungam ir svēta. Tad nu neesiet noskumuši, jo prieks pie Tā Kunga ir jūsu stiprums.
Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
11 Un tie leviti apklusināja visus ļaudis sacīdami: esiet klusu; jo šī diena ir svēta, tāpēc neesiet noskumuši.
Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
12 Tad visi ļaudis gāja ēst un dzert un daļas sūtīt un lielu prieku darīt; jo tie tos vārdus bija sapratuši, kas tiem bija sacīti.
Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
13 Un otrā dienā visas tautas cilts virsnieki, priesteri un leviti sapulcējās pie rakstu mācītāja Ezras, klausīties bauslības vārdus.
A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
14 Un tie atrada bauslībā, ka bija rakstīts, ko Tas Kungs caur Mozu bija pavēlējis, lai Israēla bērni lieveņos dzīvo pa tiem svētkiem septītā mēnesī.
Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
15 Un lai tie to izsludina un izsauc pa visām pilsētām un Jeruzālemē sacīdami: ejat ārā kalnos un atnesiet zarus no eļļas kokiem un zarus no meža eļļas kokiem un zarus no mirtu kokiem un zarus no palma kokiem un zarus no (citiem) kupliem kokiem, un taisāt lieveņus, tā kā ir rakstīts.
kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
16 Tā tie ļaudis izgāja ārā un atnesa un taisīja sev lieveņus, ikkatrs uz sava jumta un savos pagalmos un Dieva nama pagalmos un uz Ūdens vārtu lauka un uz Efraīma vārtu lauka.
Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
17 Un visa draudze, tie, kas no cietuma bija pārnākuši, taisīja lieveņus un dzīvoja lieveņos. Jo Israēla bērni nebija tā darījuši no Jozuas, Nuna dēla, laika līdz šai dienai, un tur bija varen liela līksmība.
Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
18 Un Dieva bauslības grāmata tapa ikdienas lasīta, no pirmās dienas līdz beidzamai dienai, un tie turēja svētkus septiņas dienas un astotā dienā to atsvēti, tā kā bija nolikts.
Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.