< Jozuas 14 >
1 To nu Israēla bērni iemantojuši Kanaāna zemē, ko viņiem ir izdalījuši Eleazars, tas priesteris, un Jozuas, Nuna dēls, un tie augstie Israēla bērnu cilts tēvi.
Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
2 Caur meslošanu tiem dalīja, kā Tas Kungs caur Mozu bija pavēlējis, dot tām deviņām ciltīm un tai pusciltij.
Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
3 Jo tām divām ciltīm un tai pusciltij Mozus bija devis daļu viņpus Jardānes, bet Levitiem viņš nekādu zemes daļu nebija devis viņu starpā.
Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
4 Jo Jāzepa bērnu bija divas ciltis, Manasus un Efraīms; un Levitiem nedeva nekādu īpašu daļu tai zemē, bet pilsētas vien, kur dzīvot, un ganības priekš viņu lopiem un priekš viņu īpašuma.
gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
5 Kā Tas Kungs Mozum bija pavēlējis, tā Israēla bērni darīja un izdalīja to zemi.
Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 Tad Jūda bērni piegāja pie Jozuas Gilgalā, un Kālebs, Jefunna dēls, no Ķenasa bērniem, sacīja uz viņu: tu zini to vārdu, ko Tas Kungs uz Mozu, to Dieva vīru, ir runājis Kādeš Barneā manis pēc un tevis pēc.
Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
7 Es biju četrdesmit gadus vecs, kad Mozus, Tā Kunga kalps, mani sūtīja no Kādeš Barneas, to zemi izlūkot, un es viņam atsacīju, tā kā tas bija manā sirdī.
Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
8 Bet mani brāļi, kas man bija gājuši līdz, tie darīja to ļaužu sirdi bailīgu, bet es Tam Kungam, savam Dievam, pareizi klausīju.
amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
9 Tad Mozus tai dienā zvērēja un sacīja: tā zeme, kur tu ar savu kāju esi minis, tev un taviem bērniem būs par daļu mūžam; jo tu Tam Kungam, manam Dievam, esi pareizi klausījis.
Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
10 Un nu redzi, Tas Kungs manu dzīvību ir uzturējis, tā kā Viņš ir runājis, un ir četrdesmit un pieci gadi no tā laika, kad Tas Kungs šo vārdu uz Mozu runāja, Israēlim tuksnesī staigājot, un nu redzi, es šodien esmu astoņdesmit piecus gadus vecs.
“Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
11 Es vēl šodien esmu tik stiprs, kā tai dienā kad Mozus mani izsūtīja; kāds mans spēks bija to brīdi, tāds ir mans spēks šo brīdi uz karu, uz iziešanu un ieiešanu.
Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
12 Un nu, dod man šo kalnu zemi, par ko Tas Kungs tai dienā runājis, jo tu tai dienā esi dzirdējis, ka tur dzīvo Enaķieši, un tur ir lielas stipras pilsētas; varbūt Tas Kungs būs ar mani, ka es tos varu izdzīt, tā kā Tas Kungs runājis.
Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
13 Tad Jozuas viņu svētīja un deva Kālebam, Jefunna dēlam, Hebroni par daļu.
Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
14 Tā tad Hebrone Kālebam, Jefunna dēlam, no Ķenasa bērniem, tika par daļu līdz šai dienai, tāpēc ka tas Tam Kungam, Israēla Dievam, pareizi bija klausījis.
Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
15 Bet Hebrones vārds bija vecos laikos Kiriat Arba (Arbas pilsēta), tas ir bijis viens liels cilvēks starp Enaķiešiem. Un zemei bija miers no karošanas.
(Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.