< Jonas 1 >
1 Tā Kunga vārds notika uz Jonu, Amitajus dēlu, sacīdams:
Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
2 Celies, ej uz Ninivi, to lielo pilsētu, un sludini pret to, jo viņas bezdievība ir uzkāpusi Manā priekšā.
“Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
3 Bet Jona cēlās, bēgt no Tā Kunga vaiga uz Taršišu; un viņš nogāja uz Joppi un tur atrada laivu, kas gāja uz Taršišu, un nodeva maksu un kāpa iekšā, ar tiem braukt uz Taršišu, nost no Tā Kunga vaiga.
Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
4 Bet Tas Kungs lika nākt lielam vējam jūrā, un liela vētra cēlās jūrā, tā ka tā laiva taisījās lūst.
Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
5 Tad tie laivinieki bijās un kliedza ikviens uz savu dievu un meta tos rīkus, kas laivā bija, jūrā, laivu atvieglināt no tiem. Bet Jona bija nogājis laivas apakšā un gulēja cietā miegā.
Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
6 Tad laivas virsnieks pie viņa nāca un uz viņu sacīja: ko tu guli? Celies, piesauc savu Dievu, varbūt ka tas Dievs mūs pieminēs, ka mēs neejam bojā.
Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
7 Un tie sacīja cits uz citu: iesim, metīsim meslus(lozes), lai zinām, kura dēļ šis ļaunums mums uziet? Un kad tie mesloja, tad Jona tapa iezīmēts.
Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
8 Tad tie uz viņu sacīja: saki mums jel, kādēļ šis ļaunums pār mums nāk? Kāds tavs amats un no kurienes tu nāci? Kura ir tava zeme, un no kuras tautas tu esi?
Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
9 Tad viņš uz tiem sacīja: es esmu Ebrejs un bīstos To Kungu, to debes' Dievu, kas jūru un sausumu radījis.
Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
10 Tad tie vīri bijās ar lielu bijāšanu un uz viņu sacīja: kā tu tā esi darījis? Jo tie vīri zināja, ka viņš no Tā Kunga vaiga bēga, jo viņš tiem to bija stāstījis.
Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
11 Un tie uz viņu sacīja: ko lai mēs ar tevi darām, ka jūra mums nostājās? Jo jūra palika arvienu briesmīgāka.
Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
12 Un viņš uz tiem sacīja: ņemiet mani un metiet mani jūrā, tad jūra jums nostāsies; jo es zinu, ka šī lielā vētra pār jums nāk manis dēļ.
Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
13 Bet tie vīri airēja un gribēja laivu vest malā, bet tie neiespēja, jo jūra palika arvienu briesmīgāka.
Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
14 Tad tie piesauca To Kungu un sacīja: ak Kungs, lai jel mēs neejam bojā šā vīra dvēseles dēļ, un nepielīdzini mums nenoziedzīgas asinis, jo Tu, Kungs, esi darījis, kā Tev bija pa prātam.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
15 Un tie ņēma Jonu un viņu iemeta jūrā; tad jūra nostājās no savas kaukšanas.
Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
16 Tad tie vīri bijās To Kungu ar lielu bijāšanu un upurēja Tam Kungam upurus un solīja solījumus.
Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
17 Un Tas Kungs sūtīja lielu zivi, Jonu aprīt, un Jona sabija tās zivs vēderā trīs dienas un trīs naktis.
Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.