< Jāņa Evaņg̒elijs 1 >

1 Iesākumā bija Vārds, un Vārds bija pie Dieva, un Dievs bija Vārds.
A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
2 Tas bija iesākumā pie Dieva.
Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
3 Visas lietas ir darītas caur Viņu, un bez Viņa nekas nav darīts, kas ir darīts.
Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
4 Iekš Viņa bija dzīvība, un tā dzīvība bija cilvēku gaišums.
A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
5 Un tas gaišums spīd tumsībā, un tumsība to nesaņēma.
Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Viens cilvēks bija no Dieva sūtīts, Jānis vārdā.
Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 Tas nāca liecības dēļ, ka dotu liecību par To Gaišumu, lai visi caur to ticētu.
Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
8 Viņš pats nebija tas gaišums, bet ka tas liecību dotu par To Gaišumu.
Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
9 Tam patiesam Gaišumam, kas ikvienu cilvēku apgaismo, bija nākt pasaulē.
Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
10 Viņš bija pasaulē, un pasaule ir caur Viņu darīta; bet pasaule Viņu nepazina.
Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
11 Viņš nāca pie tiem savējiem, un šie Viņu neuzņēma.
Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
12 Bet cik Viņu uzņēma, tiem Viņš deva vaļu, palikt par Dieva bērniem, tiem, kas tic uz Viņa Vārdu,
Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
13 Kas ne no asinīm, nedz no miesas gribēšanas, nedz pēc kāda vīra prāta, bet kas no Dieva dzimuši.
Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
14 Un tas Vārds tapa miesa un dzīvoja mūsu starpā, pilns žēlastības un patiesības, un mēs redzējām Viņa godību, tādu godību, kā Tā vienpiedzimušā Dēla no Tā Tēva.
Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
15 Jānis dod liecību par Viņu un sauc sacīdams: “Šis bija Tas, par ko es sacīju: kas nāk pēc manis, Tas ir bijis priekš manis. Viņš bija pirmāk nekā es.”
Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
16 Un no Viņa pilnuma mēs visi esam dabūjuši žēlastību uz žēlastību.
Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
17 Jo bauslība ir dota caur Mozu, žēlastība un patiesība ir notikusi caur Jēzu Kristu.
Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
18 Dievu neviens nekad nav redzējis: tas vienpiedzimušais Dēls, Tēva klēpī būdams, Tas mums to ir stāstījis.
Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
19 Un šī ir Jāņa liecība, kad tie Jūdi no Jeruzālemes priesterus un levitus sūtīja, lai tam jautā: “Kas tu esi?”
Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
20 Un viņš apliecināja un neliedzās, un apliecināja: “Es neesmu Kristus.”
Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
21 Un tie tam jautāja: “Kas tad? Vai tu esi Elija?” Un viņš saka: “Neesmu.” “Vai tu esi tas Pravietis?” Un viņš atbildēja: “Nē”.
Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
22 Tad tie uz viņu sacīja: “Kas tu esi? lai atbildam tiem, kas mūs sūtījuši; ko tu saki par sevi pašu?”
Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
23 Viņš sacīja: “Es esmu saucēja balss tuksnesī: sataisiet Tā Kunga ceļu, kā pravietis Jesaja sacījis.”
Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
24 Un tie izsūtītie bija no tiem farizejiem.
Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
25 Un tie viņam jautāja un uz viņu sacīja: “Kāpēc tad tu kristi, kad tu neesi Tas Kristus, nedz Elija, nedz tas Pravietis?”
“To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
26 Jānis tiem atbildēja un sacīja: “Es kristīju ar ūdeni; bet Tas jūsu vidū iestājies, ko jūs nepazīstat;
Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
27 Tas nāk pēc manis, un ir bijis priekš manis, Tam es neesmu cienīgs kurpju siksnas atraisīt.”
shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
28 Tas notika Betanijā viņpus Jardānes upes, kur Jānis kristīja.
Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
29 Otrā dienā Jānis Jēzu ierauga nākam un saka: “Redzi, Tas Dieva Jērs, kas nes pasaules grēkus.
Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
30 Šis ir Tas, par ko es esmu sacījis: pēc manis nāk vīrs, kas bijis priekš manis: jo Viņš bija pirmāk nekā es.
Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
31 Un es Viņu nepazinu: bet lai Viņš Israēlim taptu zināms, tāpēc es esmu nācis, kristīdams ar ūdeni.”
Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
32 Un Jānis deva liecību sacīdams: “Es redzēju to Garu nolaižamies no debess kā balodi un paliekam uz Viņa.
Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
33 Un es Viņu nepazinu, bet kas mani sūtījis kristīt ar ūdeni, Tas uz mani sacīja: uz ko tu redzēsi to Garu nolaižamies un paliekam, šis ir Tas, kas kristī ar Svēto Garu.
Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
34 Un es esmu redzējis un liecību devis, ka šis ir Tas Dieva Dēls.”
Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
35 Otrā dienā Jānis atkal stāvēja un divi no viņa mācekļiem,
Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
36 Un ieraudzījis Jēzu staigājam, viņš saka: “Redzi, Tas Dieva Jērs!”
suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
37 Un tie divi mācekļi viņu dzirdēja runājam un Jēzum gāja pakaļ.
Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
38 Un Jēzus atgriezdamies un tos redzējis pakaļ nākam, uz tiem saka: “Ko jūs meklējat?” Un tie uz Viņu sacīja: “Rabbi, (tas ir tulkots: mācītājs, ) kur Tu mājo?”
Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
39 Viņš uz tiem saka: “Nāciet un redziet.” Tie nāca un redzēja, kur Viņš mājoja, un palika to dienu pie Viņa, un tas bija ap desmito stundu.
Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
40 Andrejs, Sīmaņa Pētera brālis, bija viens no tiem diviem, kas to no Jāņa bija dzirdējuši un Viņam gājuši pakaļ.
Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
41 Šis pirmais atrod savu brāli Sīmani un uz to saka: “Mēs to Mesiju esam atraduši (tas ir tulkots: Kristus).”
Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
42 Un viņš to veda pie Jēzus. Un Jēzus to uzlūkoja un sacīja: “Tu esi Sīmanis, Jonas dēls, tu tapsi saukts Kefas, tas ir tulkots: Pēteris (akmens).”
Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
43 Otrā dienā Jēzus gribēja iziet uz Galileju un atrod Filipu un uz to saka: “Nāc Man pakaļ.”
Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
44 Un Filips bija no Betsaidas, Andreja un Pētera pilsētas.
Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
45 Filips atrod Natanaēli un uz to saka: “Par ko Mozus bauslībā rakstījis un tie pravieši, To mēs esam atraduši, Jēzu no Nacaretes, Jāzepa dēlu.”
Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
46 Un Natanaēls uz to sacīja: “Vai no Nacaretes var būt kāds labums?” Filips uz to saka: “Nāc un redzi!”
Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
47 Jēzus redzēja Natanaēli nākam, un par to saka: “Redzi, patiesi viens Israēlietis, iekš kā viltības nav.”
Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
48 Natanaēls uz Viņu saka: “Kā Tu mani pazīsti?” Jēzus atbildēja un uz to sacīja: “Es tevi redzēju, pirms Filips tevi aicināja, kad tu biji apakš tā vīģes koka.”
Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
49 Natanaēls atbildēja un uz Viņu saka: “Rabbi, Tu esi Dieva Dēls, Tu esi Israēla Ķēniņš.”
Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
50 Jēzus atbildēja un uz to sacīja: “Tādēļ tu tici, ka Es tev esmu sacījis: Es tevi redzēju apakš tā vīģes koka. Tu redzēsi lielākas lietas nekā tās.”
Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
51 Un Viņš uz to saka: “Patiesi, patiesi, Es jums saku: no šī laika jūs redzēsiet debesis atvērtas un Dieva eņģeļus uzkāpjam un nokāpjam uz To Cilvēka Dēlu.”
Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”

< Jāņa Evaņg̒elijs 1 >