< Jāņa Evaņg̒elijs 21 >

1 Pēc tam Jēzus tiem mācekļiem atkal parādījās pie Tiberijas jūras, un Viņš tā parādījās.
Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
2 Tur bija kopā Sīmanis Pēteris un Toms, dvīnis saukts, un Natanaēls no Kānas iekš Galilejas un tie Cebedeja dēli un divi citi no Viņa mācekļiem.
Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
3 Sīmanis Pēteris uz tiem saka: “Es iešu zvejot.” Tad tie uz viņu saka: “Mēs arī iesim tev līdz!” Tad tie izgāja un tūdaļ iekāpa laivā un nekā nedabūja tajā naktī.
Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
4 Bet kad gaisma jau bija aususi, Jēzus stāvēja malā, un tie mācekļi nezināja, to esam Jēzu.
Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
5 Tad Jēzus uz tiem saka: “Bērni, vai jums nav ko ēst?” Tie Viņam atbildēja: “Nav nekā!”
Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
6 Bet Viņš uz tiem sacīja: “Metiet tīklu pa laivas labo pusi, tad jūs atradīsiet.” Tad tie izmeta tīklu un vairs nespēja to vilkt tā pulka zivju dēļ.
Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
7 Tad tas māceklis, ko Jēzus mīlēja, uz Pēteri saka: “Tas ir Tas Kungs!” Tad Pēteris dzirdēdams, ka Tas esot Tas Kungs, drēbi apvilka (jo viņš bija noģērbies) un iemetās jūrā.
Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
8 Bet tie citi mācekļi nāca ar laivu, jo tie nebija tālu no malas, bet pie divsimt olekšu nost, un vilka to tīklu ar tām zivīm.
Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
9 Kad tie nu izkāpa pie malas, tad tie redzēja ogles liktas un zivis uz tām un maizi.
Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
10 Jēzus uz tiem saka: “Atnesiet šurp no tām zivīm, ko jūs tagad esat dabūjuši.”
Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
11 Sīmanis Pēteris iekāpa un to tīklu izvilka malā pilnu ar lielām zivīm, pusotru simts un trīs. Un jebšu to tik daudz bija, tomēr tas tīkls nesaplīsa.
Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
12 Jēzus uz tiem saka: “Nāciet un turiet azaidu.” Bet neviens no tiem mācekļiem nedrīkstēja Viņam jautāt, kas Tu esi? Jo tie gan zināja, ka Viņš bija Tas Kungs.
Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
13 Tad Jēzus nāk un to maizi ņem un tiem to dod, tā arī no tām zivīm.
Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
14 Šī nu trešā reize, ka Jēzus Saviem mācekļiem parādījies pēc Savas augšām celšanās no miroņiem.
Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
15 Kad tie nu to azaidu bija noturējuši, tad Jēzus uz Sīmani Pēteri saka: “Sīmani, Jonas dēls, vai tu Mani vairāk mīli nekā šie?” Tas uz Viņu saka: “Tiešām, Kungs, Tu zini, ka es Tevi mīlēju.” Viņš uz to saka: “Gani Manus jērus!”
Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
16 Atkal otru reiz Viņš uz to saka: “Sīmani, Jonas dēls, vai tu Mani mīli?” Tas uz Viņu saka: “Tiešām, Kungs, Tu zini, ka es Tevi mīlēju.” Viņš uz to saka: “Gani Manas avis!”
Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
17 Trešo reiz Viņš uz to saka: “Sīmani, Jonas dēls, vai tu Mani mīli?” Pēteris noskuma, ka Viņš trešo lāgu uz to sacīja: “Vai tu Mani mīli?” Un sacīja uz Viņu: “Kungs Tu visas lietas zini; Tu zini, ka es Tevi mīlēju.” Jēzus uz to saka: “Gani Manas avis!
Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
18 Patiesi, patiesi, Es tev saku: tu, jaunāks būdams, pats esi jozies un esi gājis, kur gribēdams; bet, vecs tapis, tu savas rokas izstiepsi, un cits tevi jozīs un tevi vedīs, kur tu negribi.”
Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
19 Bet to Viņš sacīja, gribēdams rādīt, ar kādu nāvi tam bija Dievu godāt. Un to runājis Viņš uz to saka: “Nāc Man pakaļ!”
Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
20 Un Pēteris apgriezies redz to mācekli, ko Jēzus mīlēja, pakaļ nākam, kas arī pie tā vakariņa pie Viņa krūtīm bija gulējis un sacījis: Kungs, kurš ir tas, kas Tevi nodos?
Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
21 Kad Pēteris to redzēja, tad viņš saka uz Jēzu: “Kungs, kas tad būs ar šo?”
Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
22 Jēzus uz to saka: “Ja Es gribu, ka šis paliek, kamēr Es nāku, kas tev par to? Nāc tu Man pakaļ!”
Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
23 Tad šī valoda cēlās starp tiem brāļiem: “Šis māceklis nemirs.” Bet Jēzus viņam nebija sacījis, ka viņš nemirs, bet: “Ja Es gribu, ka viņš paliek, kamēr Es nāku, kas tev par to?”
Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
24 Šis ir tas māceklis, kas liecību dod par šīm lietām un tās ir sarakstījis; un mēs zinām, ka viņa liecība uzticama.
Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
25 (Un vēl daudz citas lietas Jēzus ir darījis, un ja visas tās pēc kārtas uzrakstītu, tad man šķiet, ka arī visa pasaule tās sarakstītas grāmatas nevarētu saņemt. Āmen.)
Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.

< Jāņa Evaņg̒elijs 21 >