< Jesajas 62 >

1 Ciānas dēļ es klusu necietīšu un Jeruzālemes labad es nerimšu, kamēr viņas taisnība aust kā spožums un viņas pestīšana iedegās kā uguns.
Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
2 Un tautas redzēs tavu taisnību un visi ķēniņi tavu godību, un tevi sauks ar jaunu vārdu, ko Tā Kunga mute skaidri noteiks.
Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
3 Un tu būsi skaists kronis Tā Kunga rokā un ķēniņa galvas glītums tava Dieva rokā.
Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
4 Uz tevi vairs nesacīs: atstāta, un uz tavu zemi vairs nesacīs: izpostīta. Bet tevi nosauks: pie kā Man ir labs prāts, - un tavu zemi: tā laulātā. Jo Tam Kungam ir labs prāts pie tevis, un tava zeme taps laulāta.
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
5 Jo kā jauneklis laulājās ar jaunavu, tā ar tevi laulāsies tavi bērni, un kā brūtgāns priecājās par brūti, tā par tevi priecāsies tavs Dievs.
Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
6 Jeruzāleme, Es iecelšu sargus uz taviem mūriem, kas nekad ne dienu ne nakti necietīs klusu! Jūs, kas To Kungu piesaucat, nestāviet klusu!
Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
7 Neliekat Viņu mierā, kamēr Viņš stiprina Jeruzālemi un to padara slavenu virs zemes.
kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
8 Tas Kungs ir zvērējis pie Savas labās rokas un pie Sava stiprā elkoņa: Tavu labību Es vairs nedošu ēst taviem ienaidniekiem, un svešinieki nedzers vairs tavu vīnu, ar ko tu esi pūlējies.
Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
9 Bet kas to sakrāj, tie to ēdīs un slavēs To Kungu, un kas to lasīs, tie to dzers Manos svētos pagalmos.
amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
10 Izejiet, izejiet pa vārtiem, sataisiet tiem ļaudīm ceļu, līdziniet, līdziniet staigājamu ceļu, atņemiet akmeņus, izceļat karogu pār tautām.
Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
11 Redzi, Tas Kungs sludina līdz pasaules galam: sakāt Ciānas meitai: redzi, tava pestīšana nāk, redzi, Viņa alga ir pie Viņa un Viņa atmaksa ir Viņa priekšā.
Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
12 Un tos sauks: „Svētā tauta“, „Tā Kunga atpestītie“un tevi sauks „Meklētā“, „neatstātā pilsēta“.
Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.

< Jesajas 62 >