< Hozejas 13 >

1 Kad Efraīms runāja, tad cēlās bailes; viņš augsti cēlās iekš Israēla, bet viņš noziedzās caur Baālu un mira.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 Un nu tie vēl vairāk grēko, un no sava sudraba tie sev taisa elku stabus, dievekļus pēc sava prāta; tas visnotaļ ir kalēju darbs; uz tiem šie runā, cilvēku upurētāji, tie skūpsta teļus.
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 Tādēļ tie būs kā rīta mākoņi un kā rīta rasa, kas izzūd kā pelavas no klona, un kā dūmi no skursteņa top aizdzīti.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 Bet Es esmu Tas Kungs, tavs Dievs, kamēr no Ēģiptes zemes, un Dieva bez manis tu nepazīsti neviena, un Pestītāja bez Manis nav neviena.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 Es par tevi zināju tuksnesī, tai sausā zemē.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 Kad tiem bija ganība, tad tie pieēdās; kad tie bija pieēdušies, tad viņu sirds lepojās, tāpēc tie Mani aizmirsa.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 Tādēļ Es tiem paliku kā lauva, kā pardelis Es glūnēju uz ceļa.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 Es tos sastapšu kā lācis, kam bērni laupīti, un saplosīšu viņu cieto sirdi, Es tos tur aprīšu kā lauva; tie zvēri virs zemes tos saplosīs.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 Tas tev par postu, Israēl, ka tu esi pret Mani, pret savu palīgu.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 Kur nu ir tavs ķēniņš? Lai tas tev palīdz visās tavās pilsētās! Un kur tavi tiesneši, par kuriem tu sacīji: dod man ķēniņu un virsniekus?
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 Es tev devu ķēniņu savā dusmībā un to esmu atņēmis savā bardzībā.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 Efraīma noziegumi ir sakrāti, viņa grēki ir glabāti.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 Viņam nāks dzemdētājas sāpes; viņš ir negudrs bērns, jo tas laikā neiet mātes ceļā.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 Es tos atpestīšu no elles, Es tos atsvabināšu no nāves. Nāve, kur ir tavs mēris, elle, kur ir tavs posts! Žēlums nebūs priekš Manām acīm. (Sheol h7585)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
15 Lai viņš arī augļus nes brāļu vidū, bet rīta vējš nāks, Tā Kunga vējš celsies no tuksneša, un viņa aka izkaltīs, un viņa avots izsīks; šis laupīs mantu un visus dārgumus.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 Samarija ies postā, jo tā savam Dievam ir turējusies pretī, tā kritīs caur zobenu, viņu bērni taps satriekti un viņu grūtās sievas taps uzšķērstas.
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”

< Hozejas 13 >