< Pirmā Mozus 29 >
1 Un Jēkabs cēlās kājās un gāja uz to ļaužu zemi, kas pret rītiem,
Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
2 Un skatījās, un redzi, tur bija aka uz lauka. Un redzi, tur bija trīs avju pulki pie tās nometušies, jo no tās akas tās avis tapa dzirdinātas, un liels akmens bija uz akas cauruma.
A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
3 Un turpat visi avju pulki tapa sadzīti, un tie novēla to akmeni no akas cauruma un dzirdīja tās avis un uzlika atkal to akmeni uz akas caurumu savā vietā.
Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
4 Tad Jēkabs uz tiem sacīja: brāļi, no kurienes jūs esat? Un tie sacīja: mēs esam no Hāranas.
Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
5 Un viņš uz tiem sacīja: vai jūs pazīstat Lābanu, Nahora dēlu? Un tie sacīja: pazīstam gan.
Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
6 Tad viņš uz tiem sacīja: vai tam labi klājās? Un tie atbildēja: labi gan; un redzi, Rahēle, viņa meita, te nāk ar avīm.
Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
7 Un viņš sacīja: redzi, saule vēl ir gabalā, vēl nav laiks lopus pārdzīt, dzirdinājiet tās avis un ejat un paganiet tās.
Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
8 Tad tie sacīja: mēs nevaram, pirms visi avju pulki nav sadzīti; tad to akmeni noveļ no akas cauruma, un mēs dzirdinām tās avis.
Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
9 Kad viņš vēl ar tiem runāja, tad nāca Rahēle ar avīm, kas viņas tēvam piederēja, jo viņa tās ganīja.
Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
10 Un kad Jēkabs ieraudzīja Rahēli, savas mātes brāļa Lābana meitu, un savas mātes brāļa Lābana avis, tad tas piegāja un novēla to akmeni no akas cauruma un dzirdīja savas mātes brāļa Lābana avis.
Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
11 Un Jēkabs skūpstīja Rahēli un pacēla savu balsi un raudāja.
Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
12 Un Jēkabs sacīja Rahēlei, ka esot viņas tēva radinieks un Rebekas dēls, tad tā tecēja un to pasacīja savam tēvam.
Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
13 Un kad Lābans dzirdēja to vēsti par Jēkabu, savas māsas dēlu, tad tas viņam tecēja pretī un viņu apkampa un skūpstīja un ieveda savā namā. Tad tas Lābanam teica visas šās lietas.
Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
14 Un Lābans uz viņu sacīja: tiešām, tu esi no maniem kauliem un no manas miesas; un viņš pie tā palika veselu mēnesi.
Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
15 Un Lābans sacīja uz Jēkabu: jebšu tu esi mans radinieks, vai tādēļ: tu man velti kalpotu? Saki man, kādu algu tu prasi?
sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
16 Un Lābanam bija divas meitas; tās vecākās vārds bija Lea un tās jaunākās vārds bija Rahēle.
Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
17 Leas acis bija pavājas, bet Rahēle bija skaista no auguma un ģīmja.
Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
18 Un Jēkabs mīlēja Rahēli un sacīja: es tev gribu kalpot septiņus gadus par Rahēli, tavu jaunāko meitu.
Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
19 Tad Lābans sacīja: Labāki es to dodu tev, nekā citam vīram; paliec pie manis.
Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
20 Un Jēkabs kalpoja par Rahēli septiņus gadus; tās likās kādas dienas vien esam, tik mīļa tā viņam bija.
Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
21 Un Jēkabs sacīja uz Lābanu: dod man manu sievu, jo manas dienas ir pilnas, ka es pie tās eju.
Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
22 Tad Lābans sapulcēja visus tās vietas ļaudis un taisīja dzīres.
Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
23 Un vakarā viņš ņēma savu meitu Leū un to ieveda pie viņa, un Jēkabs gāja pie tās.
Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
24 Un Lābans deva savu kalponi Zilfu Leai, savai meitai, par kalponi.
Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
25 Un notikās rītā, un redzi, tā bija Lea. Tad viņš sacīja uz Lābanu: kam tu man to esi darījis? Vai es neesmu tev kalpojis par Rahēli; kam tu mani esi pievīlis?
Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
26 Tad Lābans sacīja: mūsu zemē nemēdz izdot jaunāko priekš pirmdzimtās.
Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
27 Beidz to nedēļu ar šo, tad es arī viņu tev došu par to kalpošanu, ko tu vēl citus septiņus gadus pie manis kalposi.
Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
28 Un Jēkabs tā darīja un beidza to nedēļu ar šo; tad Lābans tam deva Rahēli, savu meitu, par sievu.
Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
29 Un Lābans deva savu kalponi Bilu Rahēlei par kalponi.
Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
30 Un Jēkabs gāja arī pie Rahēles, un mīlēja Rahēli vairāk nekā Leū, un kalpoja pie Lābana vēl septiņus gadus.
Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
31 Un Tas Kungs redzēja, ka Lea netapa cienīta; tad viņš to darīja auglīgu, bet Rahēle bija neauglīga.
Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
32 Un Lea tapa grūta un dzemdēja dēlu un nosauca viņa vārdu Rūbenu; jo tā sacīja: Tas Kungs manas bēdas ir redzējis, jo nu mans vīrs mani mīļos.
Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
33 Un tā tapa atkal grūta un dzemdēja dēlu un sacīja: Tas Kungs dzirdējis, mani esam necienītu, viņš man arī šo ir devis; un tā nosauca viņa vārdu Sīmeanu.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
34 Un tā tapa atkal grūta un dzemdēja dēlu un sacīja: nu jel mans vīrs mani mīlēs; jo es viņam esmu dzemdējusi trīs dēlus. Tādēļ tā nosauca viņa vārdu Levi.
Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
35 Un viņa tapa atkal grūta un dzemdēja dēlu un sacīja: šo brīdi es slavēšu To Kungu. Tādēļ tā viņa vārdu nosauca Jūdu. Un tā mitējās dzemdēt.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.