< Pirmā Mozus 21 >
1 Un Tas Kungs piemeklēja Sāru, (it) kā viņš bija sacījis, un Tas Kungs darīja Sārai, kā bija runājis.
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 Un Sāra tapa grūta un dzemdēja Ābrahāmam dēlu viņa vecumā tai noliktā laikā, ko Dievs viņam bija sacījis.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 Un Ābrahāms nosauca sava dēla vārdu, kas viņam piedzima, ko Sāra viņam dzemdēja, Īzaku.
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 Un Ābrahāms apgraizīja savu dēlu Īzaku, astoņas dienas vecu, (it) kā Dievs tam bija pavēlējis.
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 Un Ābrahāms bija simts gadus vecs, kad tam Īzaks, viņa dēls, piedzima.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 Un Sāra sacīja: smiešanos Dievs man ir sataisījis; ikkatrs, kas to dzirdēs, par mani smiesies.
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 Un tā sacīja: kas gan Ābrahāmam būtu sacījis, ka Sāra bērnus zīdīs? Jo es esmu dzemdējusi dēlu viņa vecumā.
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 Un tas bērns auga un tapa no krūtīm atšķirts, un Ābrahāms darīja lielas dzīres tai dienā, kad Īzaks tapa atšķirts.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 Un Sāra redzēja Hāgares, tās Ēģiptietes, dēlu, ko tā Ābrahāmam bija dzemdējusi, smējēju esam;
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 Un tā sacīja uz Ābrahāmu: izdzen šo kalponi un viņas dēlu, jo šīs kalpones dēlam nebūs mantot līdz ar manu dēlu, ar Īzaku.
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 Un tas vārds Ābrahāmam ļoti rieba sava dēla dēļ.
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 Bet Dievs sacīja uz Ābrahāmu: lai tas tev neriebj tā puiša un tās kalpones dēļ. Visu, ko Sāra tev ir sacījusi, - klausi viņas balsij, jo iekš Īzaka tev dzimums taps nosaukts.
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 Tomēr arī tās kalpones dēlu Es celšu par tautu, tāpēc ka tas tavs dzimums.
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 Un no rīta agri Ābrahāms cēlās un ņēma maizi un ūdens trauku, un deva to Hāgarei, likdams uz viņas pleciem, un to bērnu; un viņš to aizraidīja; un tā gāja un maldījās Bēršebas tuksnesī.
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 Kad nu ūdens traukā pietrūka, tad tā nometa to bērnu apakš krūma,
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 Un nogāja un apsēdās tur pretī bultas šāviena tālumā, jo tā sacīja: es nevaru redzēt to bērnu mirstam; un apsēdās tur pretī un pacēla savu balsi un raudāja.
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 Un Dievs dzirdēja tā puiša balsi, un Dieva eņģelis no debesīm sauca Hāgarei un uz to sacīja: kas tev kait, Hāgare? Nebīsties, jo Dievs tā puiša balsi dzirdējis tai vietā, kur viņš ir. Celies, ņem to puisi un turi to pie savas rokas.
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 Jo Es viņu celšu par lielu tautu.
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 Un Dievs viņai atvēra acis, un tā ieraudzīja ūdens aku un gāja un pildīja to trauku ar ūdeni, un dzirdināja to puisi.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 Un Dievs bija ar to puisi, un tas auga un dzīvoja tuksnesī,
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 Un tapa strēlnieks ar stopu un dzīvoja Varanas tuksnesī; un viņa māte tam veda sievu no Ēģiptes zemes.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 Un tanī laikā Abimelehs un Pīkols, viņa karaspēka virsnieks, runāja ar Ābrahāmu sacīdami: Dievs ir ar tevi visās lietās, ko tu dari.
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 Un nu zvērē man šeitan pie Dieva, ka tu negribi viltīgs būt pret mani, nedz pret maniem bērniem, nedz pret maniem bērnu bērniem; pēc tās žēlastības, ko es tev darījis, tev būs man darīt un tai zemei, kur tu kā svešinieks piemīti.
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 Un Ābrahāms sacīja: es zvērēšu.
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 Un Ābrahāms norāja Abimelehu ūdens akas dēļ, ko Abimeleha kalpi ar varu bija paņēmuši.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 Tad Abimeleks sacīja: es nezinu, kas to darījis, ne tu man to esi sacījis, nedz es to arī esmu dzirdējis līdz šai dienai.
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 Un Ābrahāms ņēma avis un vēršus un deva tos Abimeleham, un tie abi cēla derību.
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 Bet Ābrahāms nolika savrup septiņus jērus.
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 Tad Abimelehs sacīja uz Ābrahāmu: par ko šie septiņi jēri, ko tu savrup esi nolicis?
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 Un viņš sacīja: par to, ka tev būs ņemt tos septiņus jērus no manas rokas, lai man būtu par liecību, ka es šo aku racis.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 Tāpēc tā vieta nosaukta Bēršeba, ka tie abi tur bija zvērējuši.
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 Un tie derēja derību Bēršebā. Tad cēlās Abimelehs un Pīkols, viņa karaspēka virsnieks, un griezās atpakaļ uz Fīlistu zemi.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 Bet viņš dēstīja tamariskas koku Bēršebā, un piesauca tur Tā Kunga, tā mūžīgā Dieva, vārdu.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 Un Ābrahāms piemita kā svešinieks Fīlistu zemē ilgu laiku.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.