< Pirmā Mozus 12 >

1 Un Tas Kungs sacīja uz Ābramu: izej no savas zemes un no savas dzimtenes un no sava tēva nama uz to zemi, ko Es tev rādīšu.
Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
2 Un Es tevi darīšu par lielu tautu un tevi svētīšu un darīšu tavu vārdu lielu, un tu būsi par svētību.
“Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
3 Un Es svētīšu tos, kas tevi svētī, un nolādēšu tos, kas tevi lād, un iekš tevis visas ciltis virs zemes taps svētītas.
Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
4 Un Ābrams aizgāja, kā Tas Kungs tam bija sacījis, un Lats gāja tam līdz. Un Ābrams bija septiņdesmit un pieci gadus vecs, kad viņš no Hāranas izgāja.
Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
5 Un Ābrams ņēma Sāraī, savu sievu, un Latu, savu brālēnu, un visu savu mantu, ko tie bija mantojuši, un tās dvēseles, ko tie Hāranā bija dabūjuši, un tie izgāja, ka ietu uz Kanaāna zemi, un tie nonāca Kanaāna zemē.
Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
6 Un Ābrams pārstaigāja to zemi līdz Šehemes vietai, līdz Mores ozolam; un Kanaānieši bija to laiku tai zemē.
Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
7 Tad Tas Kungs parādījās Ābramam un sacīja: tavam dzimumam Es došu šo zemi; un viņš tur uztaisīja altāri Tam Kungam, kas viņam bija parādījies.
Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
8 Un no turienes viņš cēlās uz tiem kalniem Bētelei pret rītiem, un uzcēla savu telti, ka Bētele bija pret vakariem un Aja pret austruma pusi, un uztaisīja tur Tam Kungam altāri un piesauca Tā Kunga vārdu.
Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
9 Un Ābrams cēlās un gāja iedams uz dienvidu(Negebu) pusi.
Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
10 Un tanī zemē bija bads, un Ābrams nogāja uz Ēģipti, tur mist, jo tas bads bija grūts tanī zemē.
To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
11 Un notikās, kad bija nonācis tuvu pie Ēģiptes, tad viņš sacīja uz Sāraī, savu sievu: redzi, es zinu, ka tu no vaiga esi skaista sieva.
Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
12 Un kad ēģiptieši tevi redzēs, tad tie sacīs: šī ir viņa sieva, - un mani nokaus, un tevi atstās dzīvu.
Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
13 Saki jel, ka tu mana māsa, lai man labi klājās tevis dēļ, un mana dvēsele tevis dēļ paliek dzīva.
Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
14 Kad nu Ābrams nāca Ēģiptes zemē, tad ēģiptieši redzēja to sievu, ka tā bija ļoti skaista.
Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
15 Un Faraona lielkungi viņu redzēja, un to slavēja Faraona priekšā, un tā sieva tapa ņemta Faraona namā.
Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
16 Un šis Ābramam darīja labu viņas dēļ; un tam bija avis un vērši un ēzeļi un kalpi un kalpones un ēzeļa mātes un kamieļi.
Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
17 Bet Tas Kungs mocīja Faraonu un viņa namu ar lielām mocībām, Sāraī, Ābrama sievas, dēļ.
Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
18 Tad Faraons aicināja Ābramu un sacīja: kam tu man to esi darījis? Kāpēc tu man neesi sacījis, ka šī tava sieva?
Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
19 Kāpēc tu sacīji, ka šī tava māsa? Jo es viņu sev ņēmu par sievu. Un nu redzi, še tava sieva, ņem viņu un ej.
Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
20 Un Faraons pavēlēja par viņu saviem vīriem, un tie to izvadīja un viņa sievu un visu, kas tam bija.
Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.

< Pirmā Mozus 12 >