< Ezras 5 >

1 Un pravieši Hagaja un Zaharija, Idus dēls, sludināja tiem Jūdiem, kas Jūdā un Jeruzālemē dzīvoja, - Israēla Dieva vārdā tie uz viņiem runāja.
Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
2 Tad Zerubabels, Šealtiēļa dēls, un Ješuūs, Jocadaka dēls, cēlās un sāka uzcelt Dieva namu Jeruzālemē, un līdz ar tiem tie Dieva pravieši, kas tos iedrošināja.
Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
3 Tanī laikā pie tiem atnāca Tatnajs, zemes valdītājs viņpus upes, un ŠetarBoznajs ar saviem biedriem, un uz tiem tā sacīja: kas jums atvēlējis, šo namu uztaisīt un šo mūri uzcelt?
A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
4 Tad mēs viņiem sacījām to vīru vārdus, kas šo darbu taisīja.
Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
5 Bet viņu Dieva acs bija pār Jūdu vecajiem, ka tie viņus neaizkavēja, kamēr šī lieta Dārijam nāca zināma un tie grāmatu par to dabūja atpakaļ.
Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
6 Šis ir tās grāmatas raksts, ko Tatnajs, zemes valdītājs viņpus upes, ar ŠetarBoznaju un viņa biedriem, Avarzaķiešiem, kas viņpus upes dzīvoja, rakstīja ķēniņam Dārijam.
Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
7 Tie sūtīja viņam grāmatu un tanī tā bija rakstīts: viss miers lai ir ķēniņam Dārijam.
Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
8 Ķēniņam lai ir zināms, ka mēs esam nogājuši Jūda zemē tā lielā Dieva namā, kas top uzcelts no cirstiem akmeņiem, un baļķi top ielikti sienās, un darbs top tikuši(rūpīgi) darīts un izdodas labi caur viņu rokām.
Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
9 Mēs tad esam vaicājuši tos vecajus un uz viņiem sacījuši: kas jums atvēlējis, šo namu uzcelt un šo mūri uztaisīt?
Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
10 Mēs arī viņu vārdus esam izprasījuši no tiem, tev dot ziņu un rakstīt to vīru vārdus, kas viņu virsnieki.
Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
11 Bet tie mums atdeva tādu atbildi un sacīja: mēs esam debesu un zemes Dieva kalpi un uzceļam to namu, kas jau sen priekšgados bijis uzcelts, jo liels Israēla ķēniņš to uzcēlis un pabeidzis.
Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
12 Tādēļ vien ka mūsu tēvi bija apkaitinājuši to debesu Dievu, viņš tos nodevis Kaldeja NebukadNecara, Bābeles ķēniņa, rokā, un tas šo namu nopostījis un tos ļaudis aizvedis cietumā uz Bābeli.
Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
13 Bet Bābeles ķēniņa Kirus pirmā gadā ķēniņš Kirus pavēlējis, šo Dieva namu uzcelt.
“Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
14 Un arī Dieva nama zelta un sudraba traukus, ko NebukadNecars izvedis no Dieva nama Jeruzālemē un tos novedis sava dieva namā uz Bābeli, tos ķēniņš Kirus ir ņēmis no Bābeles dieva nama, un tie ir atdoti vienam ar vārdu Šešbacars, ko viņš bija iecēlis par zemes valdītāju.
Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
15 Un viņš uz to sacīja: ņem šos traukus, ej un noved tos uz to Dieva namu, kas Jeruzālemē, un lai tas Dieva nams top uzcelts savā vietā.
ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
16 Tad šis Šešbacars nāca un lika pamatu Dieva namam Jeruzālemē, un tā no tā laika līdz šim ir strādāts, bet ne pabeigts.
“Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
17 Ja nu ķēniņam patīk, tad lai meklē ķēniņa mantu namā, kas Bābelē, vai tā ir, ka no ķēniņa Kirus pavēlēts, uzcelt Dieva namu Jeruzālemē, un lai ķēniņa pavēle par to mums top sūtīta.
Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.

< Ezras 5 >