< Ecechiela 7 >
1 Un Tā Kunga vārds uz mani notika sacīdams:
Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
2 Un tu, cilvēka bērns, tā Tas Kungs Dievs saka par Israēla zemi: gals, gals nāk pār tiem četriem zemes stūriem!
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
3 Nu nāk gals pār tevi, jo Es sūtīšu savu dusmību pret tevi, un tevi sodīšu pēc taviem ceļiem un atmaksāšu tev par visām tavām negantībām.
Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
4 Un Mana acs tevi nežēlos, un Es netaupīšu, bet Es tev darīšu pēc taviem ceļiem, un atmaksāšu tavas negantības, un jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs.
Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
5 Tā saka Tas Kungs Dievs: nelaime, redzi, nelaime vien nāk!
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
6 Gals nāk, gals nāk, tas ir uzmodies pret tevi, redzi, tas nāk!
Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
7 Tavs liktenis nāk, zemes iedzīvotājs. Laiks nāk, diena ir tuvu, troksnis, ne gaviles uz kalniem.
Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
8 Nu Es drīz gribu izgāzt Savu bardzību pār tevi un izdarīt Savu dusmību pret tevi un tevi sodīt pēc taviem ceļiem un atmaksāt tev visas tavas negantības.
Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
9 Un Mana acs nežēlos, un Es netaupīšu; pēc taviem ceļiem Es tev došu un tavas negantības Es tev atmaksāšu, un jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs, kas sit.
Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
10 Redzi, diena, redzi, tā nāk, liktenis nāk; rīkste zied, lepnība zaļo.
“‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
11 Varas darbs ir uzaudzis par rīksti bezdievībai, neviens no tiem neatliksies, neviens no viņu draudzes, neviens no viņu pulka, nekādas žēlabas par tiem.
Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
12 Laiks nāk, diena nāk. Lai pircējs nepriecājās, un pārdevējs lai nenoskumst; jo bardzība nāk pār visu viņas draudzi.
Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
13 Jo pārdevējs neatdabūs, ko pārdevis, jebšu vēl dzīvos; jo tā parādīšana nebūs velti notikusi pār visu viņas draudzi, un neviens, kas noziegumā, neizglābs savu dzīvību.
Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
14 Lai pūš ar trumetēm un visu dara gatavu, tomēr nebūs, kas ies karā; jo mana dusmība ir pār visu viņas draudzi.
“‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
15 Zobens ir ārā, un mēris un bads ir iekšā. Kas laukā, tas nomirs caur zobenu, un kas pilsētā, to aprīs bads un mēris.
A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
16 Un viņu bēgļi, kas izbēg, būs kalnos un visi vaidēs kā baloži ielejā, ikkatrs sava nozieguma dēļ.
Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
17 Visas rokas nogurs un visi ceļi sašļuks.
Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
18 Tie apvilks maisus, un bailība tos apklās, un pār visiem viņu vaigiem būs kauns un visas viņu galvas būs plikas.
Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
19 Tie izmetīs savu sudrabu uz ielām, un viņu zelts būs par sūdiem, viņu sudrabs un viņu zelts tos nevarēs izglābt Tā Kunga dusmības dienā. Ar to tie nepieēdinās savu dvēseli, nedz pildīs savu vēderu; jo tas tiem bija par apgrēcību, ka noziedzās.
“‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
20 Ar savu skaisto glītumu tie dzinuši lepnību, un no tā taisījuši savus negantos tēlus, savus riebīgos elkus. Tāpēc Es to tiem esmu darījis par sūdiem.
Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
21 Un Es to nodošu svešiem rokā par laupījumu, un bezdievīgiem virs zemes, ka tie to laupa un ka tie to sagāna.
Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
22 Un Savu vaigu Es no tiem gribu nogriezt, ka tie Manu mantu sagāna, un postītāji pār to nāks un to sagānīs.
Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
23 Taisi ķēdes, jo zeme ir pilna asins grēku, un pilsēta pilna varas darbu.
“‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
24 Tāpēc Es atvedīšu no pagāniem tos niknākos, tie viņu namus iemantos, un to vareno lepnībai Es darīšu galu, viņu svētekļi tiks sagānīti.
Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
25 Posts klāt; mieru meklēs, bet nav.
Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
26 Bēdas nāks pār bēdām un vēsts pār vēsti; tad meklēs parādīšanas no praviešiem, bet bauslība iznīks priesteriem un padoms vecajiem.
Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
27 Ķēniņš bēdāsies, un lielkungi būs apģērbti ar izbailēm, un tās zemes ļaudīm rokas nogurs. Es tiem darīšu pēc viņu ceļiem un pēc viņu nopelna Es tos gribu sodīt, un tie samanīs, ka Es esmu Tas Kungs.
Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”