< Ecechiela 22 >
1 Un Tā Kunga vārds notika uz mani sacīdams:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Tad nu, ak cilvēka bērns, vai gribi tiesāt, vai gribi tiesāt to asins pilsētu? Tad rādi viņai visas viņas negantības.
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Un saki: tā saka Tas Kungs Dievs: ak pilsēta, kas asinis izlej savā vidū, lai viņas laiks nāk, un kas sev taisa elkus un apgānās.
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 Caur tām asinīm, ko izlējusi, tu esi noziegusies, un ar saviem elkiem, ko taisījusi, tu esi sagānījusies, un tavām dienām esi likusi tuvu nākt, un esi nākusi savos gados. Tādēļ Es tevi esmu nodevis pagāniem par nievāšanu un visām zemēm par apsmieklu.
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Kas tuvu un kas tālu no tevis, tie tevi apsmies, tevi, kam vārds sagānīts un kas nekārtības pilna.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Redzi, Israēla valdnieki ikviens cik spēdams izlej asinis tavā vidū.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 Tēvu un māti tie pie tevis nicina, svešiniekam tie dara varas darbu tavā vidū, bāriņus un atraitnes tie apspiež pie tevis.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Manus svētumus tu nicini, un Manas svētās dienas tu sagāni.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 Mēlneši ir pie tevis, kas asinis izlej; tie ēd tavā vidū uz (elku)kalniem, dara bezkaunību tavā vidū.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 Tie atsedz pie tevis tēva kaunumu, un pieguļ pie tevis sārņiem nešķīstas sievas.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 Cits ar sava tuvāka sievu dara negantību, cits bezkaunīgi apgāna savu vedeklu, atkal cits atzīst savu māsu, sava tēva meitu, tavā vidū.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 Tie ņem pie tevis dāvanas, izliet asinis; tu piedzen augļus un plēs pagaidus, un esi plēsīga pie sava tuvākā ar varasdarbu, bet Mani tu esi aizmirsusi, saka Tas Kungs Dievs.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Redzi, tad Es sasitu savas rokas par to mantu, ko tu plēsi, un par tām asinīm, kas tavā vidū izlietas.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Vai tava sirds pastāvēs, vai tavas rokas būs stipras tanīs dienās, kad Es ar tevi tiesāšos? Es Tas Kungs to esmu runājis un to darīšu.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 Un Es tevi izkaisīšu starp tautām un tevi izklīdināšu pa valstīm un darīšu galu tavai nešķīstībai tavā vidū.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 Un tu būsi nesvēta caur sevi pašu priekš pagānu acīm un samanīsi, ka Es esmu Tas Kungs.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 Un Tā Kunga vārds notika uz mani sacīdams:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Cilvēka bērns! Israēla nams Man ir palicis par sārņiem, tie visi ir varš un alva un dzelzs un svins ceplī, tie ir palikuši par sudraba sārņiem.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Tādēļ tā saka Tas Kungs Dievs: Tāpēc ka jūs visi esat palikuši par sārņiem, tad redzi, Es jūs sapulcināšu Jeruzālemes vidū.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 Tā kā sudrabu un varu un dzelzi un svinu un alvu kopā liek ceplī, un uguni uzpūš apakšā, lai kausē, tā Es jūs sapulcināšu Savā dusmībā un bardzībā, un jūs ielikšu un kausēšu.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Tiešām, Es jūs sapulcināšu un uzpūtīšu pret jums Savas dusmības uguni, ka jūs tur iekšā topat kausēti.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 Tā kā sudrabs ceplī top kausēts, tāpat jūs tur tapsiet kausēti, un jūs samanīsiet, ka Es, Tas Kungs, Savu bardzību esmu izlējis pār jums.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 Un Tā Kunga vārds notika uz mani sacīdams:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 Cilvēka bērns, saki uz to: tu esi zeme, kas nav šķīstīta, kur nelīst dusmības dienā.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 Viņas pravieši cēluši dumpi viņas vidū; tā kā rūcošs lauva, kad tas laupījumu laupa, tā tie ēd dvēseles, tie plēš naudu un mantu, tie dara daudz atraitņu viņas vidū.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Viņas priesteri neganti pārkāpj manu bauslību un sagāna manus svētumus, tie neizšķir svētu un nesvētu un nemāca izšķirt, kas šķīsts un kas nešķīsts, tie apsedz savas acis priekš manām, svētām dienām, un es viņu starpā topu sagānīts.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Viņas virsnieki ir viņas vidū kā vilki, kas laupa laupījumu, izlej asinis, samaitā dvēseles, mantas kārības dēļ.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 Un viņas pravieši tos apmet ar nelīpamiem kaļķiem un redz aplamas parādīšanas un sludina tiem melus un saka: tā saka Tas Kungs Dievs; un tomēr Tas Kungs nav runājis.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 Tie ļaudis tai zemē dara varas darbu un laupīt laupa, un nabagu un bēdīgu tie plēš un svešinieku tie nospaida bez tiesas.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 Tad Es meklēju kādu vīru no tiem, kas atkal sataisītu sētu un stātos plaisumā, manā priekšā aizstāvēt to zemi, ka Es to nemaitātu, bet Es neatradu neviena.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Tāpēc Es pār tiem esmu izlējis Savu bardzību, ar Savas dusmības uguni Es tiem esmu galu darījis, viņu grēkus Es tiem esmu metis uz viņu galvu, saka Tas Kungs Dievs.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”