< Otra Mozus 19 >
1 Trešā mēnesī pēc Israēla bērnu iziešanas no Ēģiptes zemes, tanī laikā tie nonāca Sinaī tuksnesī.
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 Jo tie izgāja no Refidim un nonāca Sinaī tuksnesī un apmeta lēģeri tuksnesī; tur Israēls apmeta lēģeri pret to kalnu.
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 Un Mozus uzkāpa pie Dieva, un Tas Kungs sauca uz viņu no tā kalna un sacīja: tā tev būs sacīt uz Jēkaba namu un pasludināt Israēla bērniem:
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 Jūs esat redzējuši, ko Es ēģiptiešiem esmu darījis, ka Es jūs nesu uz ērgļu spārniem un jūs pie Sevis vedu.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 Un nu, ja jūs klausīsiet Manu balsi un turēsiet Manu derību, tad jūs no visām tautām būsiet Mans īpašums, jo Man pieder visa pasaule.
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 Un jūs Man būsiet priesteru ķēniņa valstība un svēta tauta. Šie ir tie vārdi, ko tev būs runāt uz Israēla bērniem.
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 Un Mozus nāca un sasauca ļaužu vecajus un lika viņiem priekšā visus šos vārdus, ko Tas Kungs viņam bija pavēlējis.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 Tad visi ļaudis kopā atbildēja un sacīja: visu, ko Tas Kungs ir runājis, to mēs darīsim. Un Mozus nesa to ļaužu vārdus atkal pie Tā Kunga.
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 Tad Tas Kungs sacīja uz Mozu: redzi, Es nākšu pie tevis biezā padebesī, ka tie ļaudis dzird, Mani ar tevi runājam, un ka tie arī tev tic mūžam. Un Mozus teica Tam Kungam to ļaužu vārdus.
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 Un Tas Kungs sacīja uz Mozu: ej pie tiem ļaudīm un svētī tos šodien un rītu, un lai tie mazgā savas drēbes.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 Un lai tie ir gatavi uz trešo dienu; jo trešā dienā Tas Kungs nolaidīsies priekš visu ļaužu acīm uz Sinaī kalnu.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 Un tev būs taisīt sētu ap tiem ļaudīm un sacīt: sargājaties, ka nekāpjat uz to kalnu un neaizskarat viņa galu; ikviens, kas to kalnu aizskars, tas mirdams mirs.
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 Nevienai rokai to nebūs aizskart, bet tam tik tiešām ar akmeņiem būs tapt nomētātam vai nošautam; vai tas ir lops, vai cilvēks, tam nebūs dzīvot. Kad taure atskanēs, tad tiem būs kāpt uz to kalnu.
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 Tad Mozus nonāca no tā kalna pie tiem ļaudīm. Un viņš svētīja tos ļaudis, un tie mazgāja savas drēbes.
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 Un viņš sacīja uz tiem ļaudīm: esiet gatavi uz trešo dienu, neaiztiekat sievas.
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 Un notika trešā dienā, kad gaisma ausa, tad bija pērkoni un zibeņi un biezs padebesis virs tā kalna un varen stipras bazūnes skaņa, tā ka visi ļaudis iztrūcinājās, kas bija lēģerī.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 Un Mozus tos ļaudis izveda no lēģera Dievam pretī, un tie nostājās apakšā pie tā kalna.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 Un Sinaī kalns kūpeja, tāpēc ka Tas Kungs nonāca ar uguni, un viņa dūmi cēlās tā kā krāsns dūmi, un viss kalns trīcēja ļoti.
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 Un bazūnes skaņa palika jo stipra, un Mozus runāja, un Dievs tam atbildēja caur vienu balsi.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 Kad nu Tas Kungs bija nonācis uz Sinaī kalnu, uz kalna galu, tad Tas Kungs sauca Mozu uz kalna galu, un Mozus kāpa augšām.
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 Un Tas Kungs sacīja uz Mozu: nokāp un piekodini tiem ļaudīm, lai tie cauri nelaužas redzēt To Kungu, ka daudzi no tiem nekrīt.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 Un tiem priesteriem, kas nāk pie Tā Kunga, būs svētīties, ka Tas Kungs tos nesatriec.
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 Tad Mozus sacīja uz To Kungu: tie ļaudis nevar kāpt uz Sinaī kalnu, jo Tu mums esi piekodinājis sacīdams: dari sētu ap to kalnu un svētī to.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 Tad Tas Kungs uz to sacīja: ej, kāp zemē. Tad tev un Āronam līdz ar tevi būs kāpt augšām, bet tiem priesteriem un tiem ļaudīm nebūs cauri lauzties uzkāpt pie Tā Kunga, ka Viņš tos nesatriec.
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 Tad Mozus nokāpa pie tiem ļaudīm un tiem to sacīja.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.