< Otra Mozus 17 >

1 Tad visa Israēla bērnu draudze aizgāja pa saviem gājumiem no Sina tuksneša uz Tā Kunga pavēli un apmeta lēģeri iekš Refidim, un tur nebija ūdens, tiem ļaudīm ko dzert.
Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
2 Tad tie ļaudis bārās ar Mozu un sacīja: dod mums ūdeni, ka dzeram. Tad Mozus uz tiem sacīja: ko jūs ar mani baraties? Kāpēc jūs To Kungu kārdinājat?
Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
3 Kad nu tiem ļaudīm tur pēc ūdens slāpa, tad viņi kurnēja pret Mozu un sacīja: kāpēc tu mūs esi izvedis no Ēģiptes, lai mirstam aiz slāpēm, mēs un mūsu bērni un mūsu lopi?
Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
4 Un Mozus brēca uz To Kungu un sacīja: ko lai es daru ar šiem ļaudīm? Daudz netrūkst, tad tie mani ar akmeņiem nomētās.
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
5 Tad Tas Kungs sacīja uz Mozu: ej tiem ļaudīm priekšā un ņem līdz Israēla vecajus un ņem savā rokā to zizli, ar ko tu to upi esi sitis un noej.
Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
6 Redzi, Es tur stāvēšu tavā priekšā uz klints pie Horeba, un tev būs uz to klinti sist, tad ūdens no tā iztecēs, tiem ļaudīm ko dzert. Un Mozus tā darīja priekš Israēla vecaju acīm.
Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
7 Un tās vietas vārdu nosauca Masu un Meribu (kārdināšana un strīdus), Israēla bērnu strīdus dēļ, un tāpēc ka tie To Kungu bija kārdinājuši sacīdami: vai Tas Kungs ir mūsu vidū vai nav?
Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
8 Un Amaleks nāca un kāvās ar Israēli iekš Refidim.
Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
9 Tad Mozus sacīja uz Jozua: izlasi mums vīrus un izej un kaujies pret Amaleku; rīt es stāvēšu pakalna galā, un Dieva zizlis būs manā rokā.
Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
10 Tad Jozuas darīja kā Mozus tam bija sacījis, un kāvās pret Amaleku; un Mozus un Ārons un Hurs kāpa tai pakalna galā.
Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
11 Un kamēr Mozus turēja savas rokas pacēlis, Israēls uzvarēja, un kad viņš savu roku nolaida, tad Amaleks uzvarēja.
Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
12 Bet Mozus rokas palika smagas; tad tie ņēma akmeni un lika to viņam apakšā, ka viņš uz tā sēdēja, un Ārons un Hurs turēja viņa rokas, viens vienā, otrs otrā pusē; tā viņa rokas palika stingras, kamēr saule nogāja.
Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
13 Un Jozuas Amaleku un viņa ļaudis izdeldēja caur zobena asmeni.
Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
14 Tad Tas Kungs sacīja uz Mozu: raksti to par piemiņu grāmatā, un pavēli to Jozuam ausīs; jo Es izdeldēšu Amaleka piemiņu apakš debess.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
15 Un Mozus uztaisīja altāri un nosauca viņa vārdu: Tas Kungs mans karogs,
Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
16 Un sacīja: roka pacelta pret Tā Kunga goda krēslu! Tam Kungam būs karš pret Amaleku uz bērnu bērniem!
Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”

< Otra Mozus 17 >