< Otra Mozus 10 >

1 Un Tas Kungs sacīja uz Mozu: ej pie Faraona, jo Es esmu apcietinājis viņa sirdi un viņa kalpu sirdi, lai Es šās Savas zīmes daru viņu vidū.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 Un lai tu stāsti priekš savu bērnu un bērnu bērnu ausīm, ko Es Ēģiptes zemē esmu darījis, un Manas zīmes, ko Es tur esmu cēlis, un lai jūs atzīstat, ka Es esmu Tas Kungs.
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Tad Mozus un Ārons gāja pie Faraona un uz to sacīja: tā saka Tas Kungs, tas Ebreju Dievs: cik ilgi tu liedzies pazemoties priekš Mana vaiga? Atlaid Manus ļaudis, ka tie Man var kalpot.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 Jo ja tu liegsies, atlaist Manus ļaudis, redzi, tad Es rītu vedīšu siseņus tavās robežās,
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 Un tie apklās visu zemes virsu, tā ka zemi neredzēs, un tie ēdīs to pēdējo, kas jums atlicis un palicis no krusas, un noēdīs visus jūsu kokus, kas jums zaļo laukā.
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 Un tie piepildīs tavus namus un visu tavu kalpu namus un visu ēģiptiešu namus; tādus ne tavi tēvi, ne tavu tēvu tēvi nav redzējuši no tās dienas, kamēr tie virs zemes bijuši, līdz šim; un viņš griezās un aizgāja no Faraona.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Un Faraona kalpi sacīja uz viņu: cik ilgi tas mums būs par slazda valgu? Atlaid tos ļaudis, lai tie kalpo Tam Kungam, savam Dievam; vai tu vēl neredzi, ka Ēģiptes zeme iet bojā?
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 Tad Mozus un Ārons atkal pie Faraona tapa atvesti, un viņš uz tiem sacīja: ejat un kalpojiet Tam Kungam, savam Dievam! Kas tie visi ir, kas grib noiet?
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Un Mozus sacīja: mēs iesim ar saviem jauniem un veciem, ar saviem dēliem un ar savām meitām; mēs iesim ar saviem maziem un lieliem lopiem, jo mums ir Tā Kunga svētki.
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 Tad viņš uz tiem sacīja: lai Tas Kungs jums tā palīdz, kā es jūs un jūsu bērnus atlaidīšu! Redziet, kāds ļaunums jums prātā!
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 Nē, nē, ejat jūs vīri un kalpojiet Tam Kungam, jo to jūs arī esat meklējuši. Un tos izstūma no Faraona vaiga.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 Tad Tas Kungs sacīja uz Mozu: izstiep savu roku pār Ēģiptes zemi siseņu dēļ, ka tie nāk pār Ēģiptes zemi un noēd visu zemes zāli, visu, ko krusa ir atlicinājusi.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Tad Mozus izstiepa savu zizli pār Ēģiptes zemi, un Tas Kungs deva austriņu(austruma vējš) tai zemē cauru dienu un cauru nakti; un kad rīts ausa, tad tas austriņš uzveda siseņus.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 Un siseņi uznāca pār visu Ēģiptes zemi un nolaidās visās Ēģiptes robežās lielā pulkā; priekš tiem tādu siseņu nav bijis, un pēc tiem vairs tādu nebūs.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 Jo tie apklāja visu zemes virsu, un zeme tapa aptumšota, un tie noēda visu zemes zāli un visus koku augļus, ko krusa bija atlicinājusi, un tur nepalika vairs zaļuma ne pie kokiem, ne pie lauka zāles visā Ēģiptes zemē.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Tad Faraons traucās aicināt Mozu un Āronu un sacīja: es esmu grēkojis pret To Kungu, jūsu Dievu, un pret jums.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 Un nu piedod lūdzams manus grēkus tikai šo reiz, un lūdziet To Kungu, savu Dievu, ka Viņš šo nāvi gribētu atņemt no manis.
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Un viņš aizgāja no Faraona un lūdza To Kungu.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 Tad Tas Kungs deva ļoti stipru vakara vēju; tas pacēla tos siseņus un tos iemeta niedru jūrā, ka neviens sisenis neatlika visās Ēģiptes robežās.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 Tomēr Tas Kungs apcietināja Faraona sirdi, un tas Israēla bērnus neatlaida.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Tad Tas Kungs sacīja uz Mozu: izstiep savu roku pret debesīm, ka tumsa nāk pār Ēģiptes zemi, ka tumsu var sataustīt.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Un Mozus izstiepa savu roku pret debesīm, tad cēlās bieza tumsa visā Ēģiptes zemē trīs dienas.
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 Neviens otru neredzēja, un neviens trejās dienās necēlās no savas vietas; bet visiem Israēla bērniem bija gaisma viņu mājokļos.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 Tad Faraons aicināja Mozu un sacīja: ejat, kalpojiet Tam Kungam, bet jūsu sīkiem lopiem un vēršiem būs palikt tepat; lai arī jūsu bērni iet jums līdz.
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Bet Mozus sacīja: tev būs arī mūsu rokā dot kaujamus upurus un dedzināmos upurus, ko pienest Tam Kungam, savam Dievam.
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 Mūsu lopiem arīdzan būs mums iet līdz; nevienam nadziņam nebūs palikt atpakaļ; jo no tiem mēs ņemsim, Tam Kungam, savam Dievam kalpot; jo mēs nezinām, kā mums Tam Kungam jākalpo, tiekams mēs turp nāksim.
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 Bet Tas Kungs apcietināja Faraona sirdi, un tas negribēja tos atlaist.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 Un Faraons uz viņu sacīja: ej nost no manis; sargies, ka tu vairs nenāci man priekš acīm; jo kurā dienā tu nāksi man priekš acīm, tev būs mirt.
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Tad Mozus sacīja: lai tā ir, kā tu esi sacījis; es tavu vaigu vairs neredzēšu.
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< Otra Mozus 10 >