< Piektā Mozus 15 >
1 Septītā gada galā tev būs turēt atlaišanu.
A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
2 Šāda nu ir tā atlaišana, ka ikvienam aizdevējam būs atlaist, ko tas savam tuvākam aizdevis; tam nebūs spiest savu tuvāko nedz savu brāli, jo Tam Kungam atlaišana ir izsaukta.
Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
3 No svešinieka atprasi, bet kas tev pie tava brāļa, to lai tava roka atlaiž.
Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
4 Lai jel nav nabagu tavā starpā; jo Tas Kungs svētīdams tevi svētīs tai zemē, ko Viņš, Tas Kungs, tavs Dievs, tev dos iemantot par īpašumu,
Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
5 Ja tu tikai Tā Kunga, sava Dieva, balsi klausīsi, turēdams visus šos baušļus, ko es tev šodien pavēlu.
in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
6 Jo Tas Kungs, tavs Dievs, tevi svētīs, tā kā Viņš tev runājis; tad tu aizdosi daudz tautām, bet tu neaizņemsies, un tu valdīsi pār daudz tautām, bet viņām pār tevi nebūs valdīt.
Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
7 Kad tavā starpā būs nabags, kāds no taviem brāļiem kādos vārtos tavā zemē, ko Tas Kungs, tavs Dievs, tev dos, tad tev nebūs apcietināt savu sirdi, nedz aizslēgt savu roku priekš sava nabaga brāļa;
In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
8 Bet atvērdams atver viņam savu roku un aizdodams aizdod viņam, cik viņam vajag savā trūkumā, kas trūkst.
A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
9 Sargies, ka tavā sirdī nav blēdības, ka tu nesaki: septītais gads, tas atlaišanas gads, ir tuvu, un tava acs būtu ļauna pret savu brāli, kas nabags, un tu viņam nedod; tad viņš par tevi brēks uz To Kungu, un tas tev būs par grēku.
Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
10 Dod viņam labprāt, lai tava sirds nav ļauna, kad tu viņam dod, jo tādēļ Tas Kungs, tavs Dievs, tevi svētīs visā tavā darbā un pie visa, kur tu savu roku pieliksi.
Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
11 Jo tur nabagu netrūks tai zemē, tādēļ es tev pavēlu un saku: atvērdams atver savu roku savam brālim, kas top spaidīts un ir nabags tavā zemē.
Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
12 Kad tavs brālis tev būs pārdots, Ebrejs vai Ebrejiete, tad lai viņš tev kalpo sešus gadus, bet septītā gadā tev būs viņu svabadu atlaist no sevis.
In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
13 Un kad tu viņu svabadu atlaidi, tad neatlaid viņu tukšu.
Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
14 Apdāvinādams apdāvini to no sava ganāmā pulka, no savas klēts un no sava vīna spaida; ar ko Tas Kungs, tavs Dievs, tevi svētījis, no tā tev būs viņam dot.
Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
15 Un piemini, ka tu esi bijis kalps Ēģiptes zemē, un ka Tas Kungs, tavs Dievs, tevi atpestījis, tāpēc es tev šodien pavēlu šās lietas.
Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
16 Bet ja viņš uz tevi sacīs: es no tevis negribu aiziet, tāpēc ka viņš tevi un tavu namu mīl, ka tam labi klājās pie tevis.
Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
17 Tad ņem īlenu un piedur viņa ausi pie durvīm, tad tas tev būs par kalpu mūžīgi; tāpat dari savai kalponei.
sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
18 Lai tev grūti nenākas viņu atlaist svabadu no sevis, jo sešus gadus viņš tev nokalpojis divkārtīgu algādža algu; tad tevi Tas Kungs, tavs Dievs, svētīs pie visa, ko tu darīsi.
Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
19 Ikvienu pirmdzimto, kas dzimst no tavām govīm un avīm, to tēviņu tev būs svētīt Tam Kungam, savam Dievam; ar savas govs pirmdzimto tev nebūs strādāt, un savu avju pirmdzimto tev nebūs cirpt.
Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
20 Tā Kunga, sava Dieva, priekšā tev un tavam namam to būs ēst ikgadus tai vietā, ko Tas Kungs izredzēs.
Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
21 Bet ja tam kāda vaina, ka ir vai klibs vai akls, jeb ja ir cita kāda ļauna vaina, tad tev to nebūs upurēt Tam Kungam, savam Dievam.
In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
22 Savos vārtos to ēdat, nešķīstais un šķīstais kopā, itin kā stirnu un kā briedi.
Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
23 Tikai viņa asinis tev nebūs ēst, tās tev būs izliet zemē kā ūdeni.
Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.