< Amosa 5 >
1 Klausiet šo vārdu, ar ko es par jums sāku raudu dziesmu, Israēla nams!
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 Israēla meita ir kritusi, viņa vairs necelsies, viņa ir atstāta zemē, neviena nav, kas to uzceļ.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 Jo tā saka Tas Kungs Dievs: tai pilsētai, kur iziet tūkstoši, atliksies simts, un kur iziet simts, atliksies desmit Israēla namā.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 Jo tā saka Tas Kungs uz Israēla namu: meklējiet Mani un dzīvojiet!
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 Bet nemeklējiet Bēteli un nenāciet uz Gilgalu un nenoejat uz Bēršebu, jo Gilgala taps aizvesta un Bētele paliks par neko.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Meklējiet To Kungu un dzīvojiet, - lai Viņš neizšaujas Jāzepa namā kā uguns, kas to norij, un neviens to nevar dzēst Bētelē, -
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 Jūs, kas tiesu pārvēršat par vērmelēm un stumjat taisnību pie zemes:
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 Kas radījis Sietiņu un Orijonu un nāves ēnu pārvērš par rīta gaismu un dienu aptumšo, ka nakts metās, kas jūras ūdeni sauc un to izgāž pa zemes virsu, - Kungs ir Viņa vārds,
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 Tam prāts ir, to spēcīgo postīt, ka posts nāk pār stipro pili.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 Tie ienīst to, kas vārtos pārmāca, un kas patiesību runā, to tie tur par negantu.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Tādēļ ka jūs apbēdinājāt nabagu un ņemat labības dāvanu no viņa, tad jūs gan esiet uztaisījuši namus no cirstiem akmeņiem, bet jūs tanīs nedzīvosiet, jūs esat stādījuši diženus vīna dārzus, bet viņu vīnu jūs nedzersiet.
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 Jo es zinu, ka jūsu pārkāpumu daudz un jūsu grēku varen daudz. Tie nospaida taisno un ņem dāvanas, un nomāc nabagus vārtos.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 Tādēļ prātīgais šinīs laikos cieš klusu, jo tie ir nikni laiki.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Meklējiet labu un ne ļaunu, lai jūs dzīvojat, un tā Tas Kungs, tas Dievs Cebaot, būs ar jums, kā jūs sakāt.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Ienīstiet ļaunu un mīļojiet labu un spriežat vārtos tiesu, vai varbūt Tas Kungs, tas Dievs Cebaot, neapžēlosies par Jāzepa atlikušiem.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 Tādēļ tā saka Tas Kungs, tas Dievs Cebaot, Tas Kungs: visās ielās vaimanas un visās gatvēs saka: vai, vai! Arāju sauc pie asarām, un pie vaimanām vaidētājus.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 Un visos vīna dārzos būs vaimanas, jo Es iešu caur jūsu vidu, saka Tas Kungs.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Ak vai, tiem, kas ilgojās pēc Tā Kunga dienas! Par ko tad jums būs Tā Kunga diena? Tā būs tumsa un ne gaisma.
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 Tā kā kad vīrs bēgtu no lauvas un to sastaptu lācis! Un nāktu namā un atslietos ar roku pie sienas, un čūska viņam iedzeltu!
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Vai tad Tā Kunga diena nebūs tumsa un ne gaisma, un nakts, kam nav spožuma?
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 Es ienīstu un atmetu jūsu svētkus un negribu ost jūsu sapulces.
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 Jo kad jūs Man dedzināmos upurus upurējat līdz ar saviem ēdamiem upuriem, tad Man pie viņiem nav labs prāts, un pateicības upuri no jūsu barotiem lopiem Es negribu ieredzēt.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Atstājies jel no Manis ar savu dziesmu bļaušanu, un tavu kokļu skaņu Es negribu dzirdēt.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 Bet lai plūst tiesa kā ūdens un taisnība kā stipra upe.
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Vai četrdesmit gadus tuksnesī jūs Man esat nesuši upurus un ēdamus upurus, Israēla nams?
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 Bet jūs nesāt sava(Sikuta) ķēniņa būdu un sava Ķijuna bildi, sava dieva zvaigzni, ko jūs sev pašiem bijāt taisījuši.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 Tādēļ Es jūs aizvedīšu tālu viņpus Damaskus, saka Tas Kungs, kam vārds ir Dievs Cebaot.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.