< Amosa 3 >
1 Klausiet šo vārdu, ko Tas Kungs runā uz jums, Israēla bērni, proti uz visām tām ciltīm, ko Es no Ēģiptes zemes esmu izvedis, sacīdams:
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 Es jūs vien esmu atzinis no visām zemes tautām, tādēļ Es pie jums piemeklēšu visus jūsu noziegumus.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Vai divi gan kopā staigā, ja tie papriekš nav saderējušies?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Vai lauva mežā rūc, kad viņam laupījuma nav? Vai jauns lauva balsi paceļ no savas alas, kad neko nav gūstījis?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 Vai putns iekrīt valgā pie zemes, kur valga priekš viņa nav? Vai valgs no zemes ceļas, ar ko nekas nav gūstīts?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Vai pilsētā bazūnē ar bazūni, un ļaudis neiztrūkstās? Vai kāda nelaime notiek pilsētā, ko Tas Kungs nedara?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Tiešām, Tas Kungs Dievs nekā nedara, kad viņš savu noslēpumu neparāda saviem kalpiem, tiem praviešiem.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 Kad lauva rūc, kas nebītos? Tas Kungs Dievs runā, kam nebūtu jāsludina?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Liekat to dzirdēt Ašdodas skaistos namos un Ēģiptes zemes pilīs un sakāt: sapulcinājaties uz Samarijas kalniem un redziet tos lielos trokšņus viņas vidū, un tos nospaidītos viņas starpā.
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 Jo tie nezin darīt, kas tiesa(taisnība), saka Tas Kungs, krādami netaisnību un varas darbu savās pilīs.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 Tāpēc Tas Kungs Dievs tā saka: spaidi zemei visapkārt! Un viņš nogāzīs tavu stiprumu, un tavi skaistie nami taps izpostīti.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Tā saka Tas Kungs: kā gans izrauj no lauvas rīkles divus stilbus vai kādu auss gabaliņu, tā Israēla bērni tiks izglābti, kas Samarijā sēž gultas kaktā uz Damaskus pēļa.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Klausiet un dodiet liecību Jēkaba namam, saka Tas Kungs Dievs, tas Dievs Cebaot:
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 Tai dienā, kad Es Israēla pārkāpumus pie viņa piemeklēšu, tad Es piemeklēšu Bēteles altārus, un tie altāra ragi taps nocirsti un kritīs zemē.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 Un Es sitīšu tiklab ziemas pili kā vasaras pili, un tie ziloņkaulu nami ies bojā, un daudz nami taps izpostīti, saka Tas Kungs.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.