< Apustuļu Darbi 3 >

1 Bet Pēteris un Jānis gāja kopā uz Dieva namu ap lūgšanas stundu, tā ir tā devītā.
Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
2 Un viens vīrs, no mātes miesām tizls būdams, tapa nests; to tie ikdienas nolika priekš Dieva nama durvīm, kas top sauktas tās krāšņās, ka tas dāvanas lūgtos no tiem, kas gāja Dieva namā.
Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
3 Šis, redzēdams Pēteri un Jāni, ka tie gribēja ieiet Dieva namā, lūdzās kādu dāvanu.
Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
4 Bet Pēteris ar Jāni uz to skatījās un sacīja: “Skaties uz mums.”
Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
5 Un tas skatījās uz tiem gaidīdams, ko laba no viņiem dabūt.
Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
6 Bet Pēteris sacīja: “Sudraba un zelta man nav, bet kas man ir, to es tev dodu: Jēzus Kristus no Nacaretes vārdā: celies un staigā!”
Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
7 Un viņš to satvēra pie labās rokas un to pacēla, un tūdaļ viņa lieli un krimšļi tapa stingri,
Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
8 Un uzlēcis viņš stāvēja un staigāja un gāja ar tiem Dieva namā, staigādams un lēkdams un Dievu teikdams.
Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
9 Un visi ļaudis to redzēja staigājam un Dievu teicam;
Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
10 Un to arī pazina, ka viņš tas bija, kas dāvanu dēļ pie tām Dieva nama krāšņām durvīm bija sēdējis; un tie brīnījās, iztrūcinādamies par to, kas viņam bija noticis.
Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
11 Kad nu šis tizlais, kas bija vesels tapis, pie Pētera un Jāņa turējās, tad visi ļaudis pārbijušies pie tiem satecēja tai saucamā Salamana priekšnamā.
Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
12 Bet Pēteris, to redzēdams, tiem ļaudīm atbildēja: “Jūs Israēla vīri, ko jūs brīnāties par to, jeb ko jūs lūkojieties uz mums, tā kā mēs caur savu pašu spēku un savu dievbijāšanu to būtu padarījuši, ka šis staigā?
Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
13 Ābrahāma un Īzaka un Jēkaba Dievs, mūsu tēvu Dievs, ir pagodinājis Savu Dēlu Jēzu, ko jūs esat nodevuši un aizlieguši priekš Pilatus, kad tas sprieda, Viņu laist vaļā.
Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
14 Bet jūs To Svēto un Taisno esat aizlieguši un lūguši, ka jums tas slepkava taptu dots.
Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
15 Bet To dzīvības lielkungu jūs esat nokāvuši, ko Dievs ir uzmodinājis no miroņiem; tam mēs esam liecinieki.
Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
16 Un caur to ticību uz Viņa Vārdu, Viņš pie šā, ko jūs redzat un pazīstat, Savu Vārdu ir apstiprinājis, un tā ticība, kas ir caur Viņu, šim devusi pilnīgu veselību jūsu visu priekšā.
Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
17 Un nu brāļi, es zinu, ka nezinādami to esat darījuši, jūs kā arī jūsu virsnieki.
Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
18 Bet ko Dievs caur visu Savu praviešu muti papriekš sludinājis, ka Kristum bija ciest, to Viņš tā ir piepildījis.
Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
19 Tāpēc atjaunojaties savā prātā un atgriežaties, ka jūsu grēki top izdeldēti, lai atspirgšanas laiki nāk no Tā Kunga vaiga,
Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
20 Un lai Viņš Jēzu Kristu sūta, kas jums papriekš ir sludināts,
domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
21 Ko debesīm būs uzņemt līdz tam laikam, kad viss būs atjaunots, par ko Dievs jau sen ir runājis caur visu Savu svēto praviešu muti. (aiōn g165)
Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn g165)
22 Jo Mozus uz tiem tēviem ir sacījis: Tas Kungs jūsu Dievs jums cels vienu pravieti no jūsu brāļiem tā kā mani; To jums būs klausīt visās lietās, ko Tas uz jums runās.
Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
23 Un notiks, ka ikkatra dvēsele, kas neklausīs šim Pravietim, taps izdeldēta no tiem ļaudīm.
Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
24 Un visi pravieši no Samuēla sākot, un visi, kas pēc ir runājuši, tie arī šās dienas ir pasludinājuši.
I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
25 Jūs esat to praviešu un tās derības bērni, (tās derības), ko Dievs darījis ar mūsu tēviem sacīdams uz Ābrahāmu: caur tavu sēklu visas ciltis virs zemes taps svētītas.
Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
26 Dievs, Savu bērnu Jēzu uzmodinājis, To papriekš pie jums ir sūtījis, lai Tas jūs svētītu, ka ikviens atgrieztos no sava ļaunuma.”
Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”

< Apustuļu Darbi 3 >