< Otra Ķēniņu 5 >
1 Un Naēmans, Sīrijas ķēniņa kara lielskungs, bija augsts vīrs priekš sava kunga un no lielas slavas; jo caur viņu Tas Kungs Sīriešiem bija devis laimi, un viņš bija varens vīrs, bet spitālīgs.
Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
2 Un no Sīrijas sirotāji bija izgājuši un aizveduši no Israēla zemes mazu meiteni, kas bija Naēmana sievas kalpone.
To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
3 Un tā sacīja uz savu valdnieci: kaut mans kungs būtu pie tā pravieša, kas Samarijā, tas viņu gan atsvabinātu no spitālības.
Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
4 Un (Naēmans) gāja un to teica savam kungam sacīdams: tā un tā, tā meitene runājusi, kas ir no Israēla zemes.
Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
5 Tad Sīrijas ķēniņš sacīja: ej, es sūtīšu grāmatu Israēla ķēniņam. Un tas gāja un ņēma līdz desmit talentus sudraba un seštūkstoš sēķeļus zelta un desmit svētku drēbes.
Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
6 Un viņš nesa to grāmatu Israēla ķēniņam, kur bija rakstīts: kad šī grāmata pie tevis nāk, redzi, tad es savu kalpu Naēmanu pie tevis esmu sūtījis, lai tu viņu atsvabini no viņa spitālības.
Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
7 Kad nu Israēla ķēniņš šo grāmatu bija lasījis, tad viņš saplēsa savas drēbes un sacīja: vai tad es esmu Dievs, ka varu nokaut un atkal dzīvu darīt, ka šis pie manis sūta vīru, lai to atsvabinu no viņa spitālības? Ņemiet vērā un redziet, ka tas iemeslus pie manis meklē.
Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
8 Bet kad Eliša, tas Dieva vīrs, to dzirdēja, ka Israēla ķēniņš savas drēbes bija saplēsis, tad viņš sūtīja pie ķēniņa un lika sacīt: kāpēc tu savas drēbes esi saplēsis? Lai jel viņš nāk pie manis un atzīst, pravieti esam iekš Israēla.
Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
9 Un Naēmans ar saviem zirgiem un ar saviem ratiem nāca un apstājās priekš Elišas nama durvīm.
Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
10 Un Eliša sūtīja vēstnesi pie tā un lika sacīt: ej un mazgājies septiņas reizes Jardānē, tad tava miesa atkal būs vesela, un tu tapsi šķīsts.
Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
11 Bet Naēmans apskaitās un aizgāja un sacīja: redzi, es domāju, viņš taču nāks pie manis ārā un stāvēs un piesauks Tā Kunga, sava Dieva, vārdu un ar savu roku braucīs pār to vietu un atņems to spitālību.
Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
12 Vai Amana un Farfara, tās upes pie Damaskus, nav labākas nekā visi Israēla ūdeņi, vai es tur nevaru mazgāties, lai topu šķīsts? Un viņš griezās atpakaļ un aizgāja dusmās.
Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
13 Tad viņa kalpi piegāja un ar to runāja un sacīja: mans tēvs, kad tas pravietis tev būtu teicis kādu lielu lietu, vai tu to nedarītu? Kā nu ne, kad viņš tev sacījis: mazgājies, tad tu tapsi šķīsts.
Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
14 Tad viņš nokāpa un mazgājās Jardānē septiņas reizes pēc Tā Dieva vīra vārda, un viņa miesa palika atkal vesela, kā maza bērna miesa, un viņš tapa šķīsts.
Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
15 Tad viņš griezās atpakaļ pie Tā Dieva vīra ar visu savu pulku un nāca un apstājās priekš tā un sacīja: redzi, nu es zinu, ka cita Dieva nav pa visu pasauli kā vien iekš Israēla. Un nu ņem lūdzams kādu svētību no sava kalpa.
Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
16 Bet tas sacīja: tik tiešām kā Tas Kungs dzīvs, priekš ka es stāvu, es to neņemšu. Un viņš tam uzstājās, lai ņemot, bet tas liedzās.
Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
17 Tad Naēmans sacīja: Ja ne, tad ļauj jel dot savam kalpam divu zirgēzeļu nastas zemes. Jo tavs kalps svešiem dieviem vairs nenesīs ne dedzināmus upurus ne kaujamus upurus, kā vien Tam Kungam.
Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
18 Šinī lietā lai Tas Kungs tavam kalpam piedod, kad mans kungs ies Rimona namā tur pielūgt un viņš atspiedīsies uz manu roku, un es nometīšos Rimona namā, tad lai Tas Kungs tavam kalpam piedod šo lietu, kad es tā nometos Rimona namā.
Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
19 Un viņš uz to sacīja: ej ar mieru.
Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
20 Kad nu viņš kādu ceļa gabalu no tā bija aizgājis, tad Gehazis, Elišas, Tā Dieva vīra, puisis, domāja: redzi, mans kungs šo Sīrieti Naēmanu ir saudzējis un no viņa rokas neko nav ņēmis no tā, ko viņš atnesis; tik tiešām kā Tas Kungs dzīvs, es tam skriešu pakaļ un ņemšu ko no viņa.
sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
21 Tā Gehazis skrēja Naēmanam pakaļ, un kad Naēmans redzēja, sev pakaļ skrienam, tad viņš nokāpa no saviem ratiem viņam pretī un sacīja: vai viss labi?
Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
22 Un tas sacīja: labi. Mans kungs mani sūtījis un liek sacīt: redzi, tagad divi puiši no praviešu bērniem pie manis atnākuši no Efraīma kalniem, dod jel viņiem talentu sudraba un divas svētku drēbes.
Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
23 Un Naēmans sacīja: ņem lūdzams divus talentus. Un tas tam uzstājās un iesēja divus talentus sudraba divos makos un divas svētku drēbes, un tos deva diviem no saviem puišiem, kas tos viņa priekšā nonesa.
Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
24 Kad nu viņš nāca pie pakalnes, tad viņš to paņēma no viņu rokām un to nolika namā un tos vīrus atlaida, ka tie aizgāja.
Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
25 Bet viņš nāca un tur stāvēja sava kunga priekšā. Un Eliša uz to sacīja: kur tu biji, Gehazi? Un tas sacīja: tavs kalps ne šur ne tur nav bijis.
Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
26 Bet viņš uz to sacīja: vai mana sirds tur līdzi nestaigāja, kad tas vīrs griezās atpakaļ no saviem ratiem tev pretī? Vai tas bija laiks, ņemt sudrabu un drēbes un eļļas kokus un vīna dārzus un avis un vēršus un kalpus un kalpones?
Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
27 Tāpēc Naēmana spitālība tev pielips un tavam dzimumam mūžam. Tad tas no viņa aizgāja spitālīgs kā sniegs.
Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.