< Otra Ķēniņu 3 >

1 Un Jorams, Ahaba dēls, palika par ķēniņu pār Israēli Samarijā, Jehošafata, Jūda ķēniņa, astoņpadsmitā gadā un valdīja divpadsmit gadus.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, bet ne tā, kā viņa tēvs un kā viņa māte, jo viņš lika noņemt to uzcelto Baāla stabu, ko viņa tēvs bija taisījis.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Tikai viņš pieķērās Jerobeama, Nebata dēla, grēkiem, uz ko tas Israēli bija pavedis, - no tiem viņš neatstājās. -
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Un Mešum, Moaba ķēniņam, bija daudz lopu, un viņš deva Israēla ķēniņam par mesliem simts tūkstoš jērus un simts tūkstoš aunus ar visu vilnu.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 Bet kad Ahabs bija nomiris, tad Moaba ķēniņš atkrita no Israēla ķēniņa.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Tad ķēniņš Jorams tai laikā cēlās no Samarijas un sarīkoja visu Israēli,
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 Un nogāja un sūtīja pie Jehošafata, Jūda ķēniņa, sacīdams: Moaba ķēniņš no manis atkritis, vai tu līdz ar mani gribi karā iet pret Moabu? Un tas sacīja: es iešu līdz, es būšu kā tu, mani ļaudis kā tavi ļaudis, un mani zirgi kā tavi zirgi.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Un viņš sacīja: pa kuru ceļu iesim? Un tas sacīja pa Edoma tuksneša ceļu.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Tā tie gāja, Israēla ķēniņš un Jūda ķēniņš un Edoma ķēniņš. Un kad tie bija gājuši septiņu dienu gājumu, tad tiem nebija ūdens, ne karaspēkam, ne lopiem, kas tiem bija līdz.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Tad Israēla ķēniņš sacīja: Ak vai! Tas Kungs šos trīs ķēniņus aicinājis, ka Viņš tos dotu Moaba rokā!
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Un Jehošafats sacīja: vai še nav kāds no Tā Kunga praviešiem, ka To Kungu caur viņu vaicātu? Tad viens no Israēla ķēniņa kalpiem tam atbildēja un sacīja: še ir Eliša, Šafata dēls, kas ūdeni lēja uz Elijas rokām.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 Un Jehošafats sacīja: Tā Kunga vārds ir pie viņa. Tad pie tā nogāja Israēla ķēniņš un Jehošafats un Edoma ķēniņš.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Bet Eliša sacīja uz Israēla ķēniņu: kas man ar tevi? Ej pie sava tēva praviešiem un pie savas mātes praviešiem. Bet Israēla ķēniņš uz to sacīja: nē, jo Tas Kungs šos trīs ķēniņus ir aicinājis, ka viņš tos dotu Moaba rokā.
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Un Eliša sacīja: tik tiešām kā Tas Kungs Cebaot dzīvs, priekš kā es stāvu, ja es to nedarītu Jehošafata, Jūda ķēniņa, labad, tad es tev ne virsū neskatītos nedz tevi ievērotu.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Nu tad, dabūjat man vienu koklētāju. Un tam koklētājam koklējot Tā Kunga roka nāca pār viņu,
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 Un viņš sacīja: tā saka Tas Kungs: rokat grāvi pie grāvja šinī ielejā.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Jo tā saka Tas Kungs: jūs neredzēsiet ne vēju ne lietu, tomēr šī ieleja būs pilna ūdens, jums dzert pašiem un jūsu sīkiem un lieliem lopiem.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Un tas ir vēl maz priekš Tā Kunga, viņš arī Moabu dos jūsu rokā.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 Un jums būs kaut visas stiprās pilsētas un visas izredzētās pilsētas, un nocirst visus labos kokus un aizbāzt visus ūdens avotus un samaitāt visus labos tīrumus ar akmeņiem.
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Un notikās no rīta ap ēdamā upura laiku, redzi, tad ūdens nāca no Edoma puses, un zeme tapa ūdens pilna.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Kad nu visi Moabieši dzirdēja, ka tie ķēniņi nāca, pret tiem karot, tad tie sasauca visus, kas spēja bruņas nest, un vēl pārāki(vecākie) un tie stājās uz robežām.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Un kad tie no rīta agri cēlās un saule bija uzlēkusi pār to ūdeni, tad Moabieši no tālienes to ūdeni redzēja sarkanu kā asinis.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 Un tie sacīja: tās ir asinis; tiešām tie ķēniņi pacēluši zobenu, zobenus viens pret otru un cits citu nokāvuši. Un nu, Moab, celies uz laupīšanu.
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Bet kad tie nāca pie Israēla lēģera, tad Israēlieši cēlās un kāva Moabiešus un šie no viņiem bēga. Un tie tur ielauzās un apkāva Moabiešus,
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 Un nopostīja tās pilsētas, un ikkatrs meta savu akmeni uz visiem labiem tīrumiem un tos sameta pilnus, un aizbāza visus avotus un nocirta visus labos kokus, līdz kamēr Ķirarezetē akmeņus vien atlicināja. Un lingotāji ap to apmetās un tai svieda virsū.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Kad nu Moaba ķēniņš redzēja, ka kaušanās tam metās par stipru, tad viņš pie sevis ņēma septiņsimt vīrus, kas zobenu izvilka, lauzties cauri pret Edoma ķēniņu, bet tie nespēja.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Tad viņš ņēma savu pirmdzimušo dēlu, kam viņa vietā bija palikt par ķēniņu, un to upurēja par dedzināmo upuri uz mūra. Un Israēli pārņēma lielas dusmas un tie no tā atstājās un griezās atpakaļ uz savu zemi.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< Otra Ķēniņu 3 >