< Otra Ķēniņu 23 >

1 Tad ķēniņš sūtīja, un pie viņa sapulcinājās visi vecaji no Jūda un Jeruzālemes.
Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
2 Un ķēniņš gāja Tā Kunga namā un līdz ar viņu visi Jūda vīri un visi Jeruzālemes iedzīvotāji un visi priesteri un pravieši un visi ļaudis, gan mazi, gan lieli. Un viņš lasīja priekš viņu ausīm visus vārdus no tās derības grāmatas, kas bija atrasta Tā Kunga namā.
Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
3 Un ķēniņš stāvēja tai augstajā vietā un derēja derību priekš Tā Kunga vaiga, Tam Kungam pakaļ staigāt un turēt Viņa baušļus un Viņa liecības un Viņa likumus no visas sirds un no visas dvēseles, stipri turēt šās derības vārdus, kas bija rakstīti šai grāmatā. Un visi ļaudis uzņēma šo derību.
Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
4 Un ķēniņš pavēlēja augstajam priesterim Hilķijam, un otras kārtas priesteriem un sliekšņa sargiem, iznest no Tā Kunga nama visus rīkus, kas bija taisīti Baālam un Ašerai un visam debess pulkam, un viņš tos sadedzināja ārā aiz Jeruzālemes Kidronas ielejā un viņu pīšļus lika nest uz Bēteli.
Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
5 Viņš arī nocēla tos kalnu priesterus, ko Jūda ķēniņi bija iecēluši, kvēpināt uz kalniem Jūda pilsētas un ap Jeruzālemi, arī tos, kas kvēpināja Baālam, saulei un mēnesim un zvaigznēm un visam debess pulkam.
Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
6 Viņš arī izmeta to Ašeru no Tā Kunga nama ārā aiz Jeruzālemes pie Kidronas upes un to sadedzināja pie Kidronas upes un to sagrūda pīšļos un nometa viņas pīšļus uz ļaužu bērnu kapiem.
Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
7 Viņš noplēsa arī maucinieku namus, kas pie Tā Kunga nama bija, kur sievas auda teltis priekš Ašeras.
Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
8 Un viņš saaicināja visus priesterus no Jūda pilsētām un sagānīja tos kalnu altārus, kur tie svētītāji bija kvēpinājuši, no Ģebas līdz Bēršebai, un noplēsa elku altārus pie vārtiem, to, kas bija Jozuas, pilsētas virsnieka, vārtu priekšā, (un to, kas) bija pa kreiso roku, kad ieiet pilsētas vārtos.
Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
9 Bet kalnu priesteri neupurēja uz Tā Kunga altāra Jeruzālemē, bet tie ēda neraudzētu maizi starp saviem brāļiem.
Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
10 Viņš sagānīja arī Tovetu, Inoma bērnu ielejā, ka neviens savam dēlam vai meitai neliktu caur uguni iet Molokam.
Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
11 Viņš arī atmeta tos zirgus, ko Jūda ķēniņi saulei bija cēluši, kur Tā Kunga namā iet, pie kambarjunkura NetanMeleka kambara, kas iekš Parvarim, un sadedzināja arī saules ratus ar uguni.
Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
12 Viņš noplēsa arī tos altārus, kas bija uz Ahaza augšistabas jumta, ko Jūda ķēniņi bija taisījuši līdz ar tiem altāriem, ko Manasus bija taisījis Tā Kunga nama abos pagalmos, un tos sagrūda un meta viņu pīšļus Kidronas upē.
Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
13 Un ķēniņš sagānīja tos kalnu altārus Jeruzālemes priekšā, pa labo roku samaitāšanas kalnam, ko Salamans, Israēla ķēniņš, bija uztaisījis Astartei, Sidona negantībai, un Kamosam, Moaba negantībai, un Milkonam, Amona bērnu negantībai.
Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
14 Un viņš sadragāja tos stabus un nopostīja tās Ašeras un pildīja viņu vietas ar cilvēku kauliem.
Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
15 Viņš noplēsa arī to altāri, kas bija Bētelē, to kalna namu, ko Jerobeams, Nebata dēls, bija taisījis, kas Israēli paveda uz grēkiem: to altāri un kalna namu viņš noplēsa un sadedzināja to kalna namu un to sagrūda pīšļos un sadedzināja to Ašeru.
Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
16 Un Josija apgriezās un redzēja tos kapus, kas tur tanī kalnā bija; un viņš sūtīja un ņēma tos kaulus no tiem kapiem un tos sadedzināja uz tā altāra un to sagānīja pēc Tā Kunga vārda, ko tas Dieva vīrs bija sludinājis, kas šīs lietas sludināja.
Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
17 Un viņš sacīja: kas tā par kapa zīmi, ko es redzu? Un tās pilsētas ļaudis uz to sacīja: Tas ir Tā Dieva vīra kaps, kas no Jūda atnāca un šās lietas pasludināja, ko tu pie Bēteles altāra darījis.
Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
18 Un viņš sacīja: Lai tas dus mierā, neviens lai neaiztiek viņa kaulus. Tā tie izglāba viņa kaulus ar tā pravieša kauliem, kas no Samarijas bija nācis.
Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
19 Josija arī noplēsa visus kalnu namus Samarijas pilsētās, ko Israēla ķēniņi bija cēluši, to (Kungu) kaitinādami, un viņš tiem darīja, kā viņš Bētelē bija darījis.
Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
20 Un visus kalnu priesterus, kas tur bija, viņš nokāva uz tiem altāriem un sadedzināja cilvēku kaulus uz tiem; tad viņš griezās atpakaļ uz Jeruzālemi.
Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
21 Un ķēniņš pavēlēja visiem ļaudīm sacīdams: turat Tam Kungam, savam Dievam, Pasa svētkus, kā šīs derības grāmatā rakstīts.
Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
22 Jo tādi Pasa svētki kā šie nebija turēti nedz soģu laikā, kas Israēli tiesāja, nedz visu Israēla ķēniņu, nedz Jūda ķēniņu laikā;
Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
23 Bet ķēniņa Josijas astoņpadsmitā gadā šie Pasa svētki Tam Kungam tapa turēti Jeruzālemē.
Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
24 Un Josija arī izdeldēja pūtējus un burvjus, tēlus un elkus un visu negantību, ko vien redzēja Jūda zemē un Jeruzālemē, ka viņš stipri turētu bauslības vārdus, kas bija rakstīti tai grāmatā, ko priesteris Hilķija bija atradis Tā Kunga namā.
Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
25 Un priekš viņa nebija tāds ķēniņš, kā viņš, kas pie Tā Kunga būtu atgriezies no visas savas sirds un no visas savas dvēseles un ar visu savu spēku, pēc visas Mozus bauslības, un arī pēc viņa tāds necēlās, kā viņš.
Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
26 Tomēr Tas Kungs negriezās no Savas lielās dusmības karstuma, ar ko Viņa bardzība pret Jūdu bija iedegusies, par visu kaitināšanu, ar ko Manasus Viņu bija kaitinājis.
Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
27 Un Tas Kungs sacīja: Es atmetīšu arī Jūdu nost no Sava vaiga, kā Es Israēli esmu atmetis, un atmetīšu šo pilsētu, ko Es biju izredzējis, proti Jeruzālemi, un to namu, par ko biju sacījis: Mans vārds tur būs.
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
28 Un kas vēl par Josiju stāstāms un viss, ko viņš darījis, tas rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
29 Viņa laikā Faraons Nekus, Ēģiptes ķēniņš, cēlās pret Asīrijas ķēniņu pie Eifrat upes. Un ķēniņš Josija tam gāja pretī, un Ēģiptes ķēniņš to nokāva pie Meģidus, kad tie sastapās.
Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
30 Un viņa kalpi to aizveda nomirušu no Meģidus un to noveda uz Jeruzālemi un to apraka viņa kapā. Un tās zemes ļaudis ņēma Joakasu, Josijas dēlu, un to svaidīja un cēla par ķēniņu viņa tēva vietā.
Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
31 Joakas bija divdesmit un trīs gadus vecs, kad viņš palika par ķēniņu, un valdīja trīs mēnešus Jeruzālemē. Un viņa mātei bija vārds Amutala, Jeremijas meita no Libnas.
Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
32 Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, kā viņa tēvi bija darījuši.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
33 Bet Faraons Nekus to saistīja Riblatā, Hamatas zemē, lai nebūtu vairs par ķēniņu Jeruzālemē, un viņš uzlika zemei meslus dot, simts talentus sudraba un vienu talentu zelta.
Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
34 Un Faraons Nekus iecēla par ķēniņu Elijaķimu, Josijas dēlu, viņa tēva Josijas vietā, un viņam deva citu vārdu, Jojaķimu. Bet Joakasu viņš ņēma līdz, un tas nāca uz Ēģipti un tur nomira.
Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
35 Un Jojaķims Faraonam deva sudrabu un zeltu. Bet viņš lika zemi uzrakstīt, lai varētu to sudrabu dot pēc Faraona pavēles, no ikkatra pēc tā raksta viņš to zeltu un sudrabu piedzina no zemes ļaudīm, ko dot Faraonam Nekum.
Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
36 Jojaķims bija divdesmit pieci gadus vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja vienpadsmit gadus Jeruzālemē. Un viņa mātei bija vārds Zebuda, Pedajus meita, no Rumas.
Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
37 Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, kā viņa tēvi bija darījuši.
Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.

< Otra Ķēniņu 23 >