< Otra Ķēniņu 21 >
1 Manasus bija divpadsmit gadus vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja piecdesmit un pieci gadus Jeruzālemē. Un viņa mātei bija vārds Evciba.
Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
2 Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, pēc to pagānu negantības, ko Tas Kungs bija izdzinis Israēla bērnu priekšā.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Jo tas uztaisīja atkal kalnu altārus, ko viņa tēvs Hizkija bija iznīcinājis, un cēla Baālam altārus un taisīja Ašeru, kā Ahabs, Israēla ķēniņš, bija darījis, un metās zemē priekš visa debesspulka un tiem kalpoja.
Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
4 Viņš taisīja arī altārus Tā Kunga namā, par ko Tas Kungs sacījis: “Jeruzālemē Es gribu likt Savu Vārdu.”
Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
5 Viņš uztaisīja altārus arī visam debess pulkam abos Tā Kunga nama pagalmos.
Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
6 Un viņš lika savam dēlam iet caur uguni un cienīja zīlēšanu un vārdošanu un pieturēja pūtējus un burvjus, un darīja daudz ļauna priekš Tā Kunga acīm, Viņu kaitinādams.
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
7 Viņš arī lika Ašeras bildi, ko bija taisījis, tai namā, par ko Tas Kungs bija sacījis uz Dāvidu un viņa dēlu Salamanu: šai namā un Jeruzālemē, ko Es no visām Israēla ciltīm izredzējis, Es Savu vārdu likšu mūžīgu
Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Un Israēla kājai Es vairs nelikšu kustēt no tās zemes, ko Es esmu devis viņu tēviem, kad tie tura un dara visu, ko Es tiem esmu pavēlējis, un visu bauslību, ko Mans kalps Mozus tiem pavēlējis.
Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
9 Bet tie neklausīja, jo Manasus tos apmaldināja, ka tie ļaunāki darīja nekā tie pagāni, ko Tas Kungs Israēla bērnu priekšā bija izdeldējis.
Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 Tad Tas Kungs runāja caur Saviem kalpiem, tiem praviešiem, un sacīja:
Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
11 Tāpēc ka Manasus, Jūda ķēniņš, darījis šādu negantību, ļaunāki pār visu, ko Amorieši darījuši priekš viņa, un Jūdu arīdzan pavedis uz grēkiem caur saviem elkudieviem,
“Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
12 Tāpēc Tas Kungs, Israēla Dievs tā saka: redzi, Es vedīšu nelaimi pār Jeruzālemi un pār Jūdu, ka ikkatram, kas to dzird, abas ausis skanēs.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
13 Jo Es Jeruzālemi izdalīšu kā Samariju un izsvēršu kā Ahaba namu, un izslaucīšu Jeruzālemi, kā bļodu izslauka, kas top izslaucīta un uz muti apgāzta.
Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
14 Un Es atmetīšu Savas tautas atlikušos un tos nodošu viņu ienaidnieku rokā, un tie būs par laupījumu un izpostījumu visiem saviem ienaidniekiem.
Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
15 Tāpēc ka tie darījuši, kas Man nepatīk, un Mani apkaitinājuši no tās dienas, kad viņu tēvi izgāja no Ēģiptes, līdz šai dienai.
domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
16 Un Manasus arī izlēja daudz nenoziedzīgas asinis, tiekams Jeruzāleme tapa pilna no viena gala līdz otram, pāri par to grēku, uz ko viņš Jūdu paveda, darīt, kas Tam Kungam nepatika.
Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
17 Un kas vēl par Manasu stāstāms un viss, ko viņš darījis un viņa grēki, ko viņš grēkojis, tas viss ir rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
18 Un Manasus aizmiga saviem tēviem pakaļ un tapa aprakts sava nama dārzā, Uzas dārzā, un viņa dēls Amons palika par ķēniņu viņa vietā.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
19 Amons bija divdesmit un divus gadus vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja divus gadus Jeruzālemē. Un viņa mātei bija vārds Mezulemeta, Aruca meita, no Jotbas.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
20 Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, kā viņa tēvs Manasus bija darījis.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
21 Un viņš staigāja visos tanīs ceļos, kur viņa tēvs bija staigājis, un kalpoja tiem elkadieviem, kam viņa tēvs bija kalpojis, un metās zemē priekš tiem.
Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
22 Un viņš atstāja To Kungu, savu tēvu Dievu, un nestaigāja Tā Kunga ceļos.
Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
23 Un Amona kalpi cēla dumpi pret viņu un nokāva ķēniņu viņa namā.
Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
24 Bet tās zemes ļaudis kāva visus, kas dumpi bija cēluši pret ķēniņu Amonu. Un tie zemes ļaudis darīja viņa dēlu Josiju par ķēniņu viņa vietā.
Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
25 Un kas vēl par Amonu stāstāms, ko viņš darījis, tas viss ir rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
26 Un viņš savā kapā tapa aprakts Uzas dārzā, un viņa dēls Josija palika par ķēniņu viņa vietā.
Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.