< Pirmā Samuela 22 >

1 Tad Dāvids aizgāja no turienes un bēga uz Adulama alu. Un viņa brāļi to dzirdēja ar visu viņa tēva namu un nonāca pie viņa uz turieni.
Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
2 Un pie viņa sapulcinājās visi vīri, kas bija spaidos, un visi, kam bija daudz parādu, un visi, kam bija rūgtums sirdī, un viņš tiem palika par virsnieku, un pie viņa bija pie četrsimt vīru.
Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
3 Un Dāvids gāja no turienes uz Micpu Moaba zemē, un sacīja uz Moaba ķēniņu: lai jel mans tēvs un mana māte pie jums dzīvo, tiekams es atzīšu, ko Dievs ar mani darīs.
Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
4 Un viņš tos noveda pie Moaba ķēniņa un tie palika pie tā, kamēr Dāvids mita kalnos.
Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
5 Tad pravietis Gads sacīja uz Dāvidu: nepaliec uz šiem kalniem, ej un paliec Jūda zemē. Tad Dāvids gāja un nāca Areta mežā.
Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
6 Un Sauls dzirdēja, ka Dāvids bija pamanīts ar tiem vīriem, kas pie viņa bija. Un Sauls sēdēja pie Ģibejas apakš kupla koka uz kalna, un viņa šķēps bija viņa rokā, un visi viņa kalpi stāvēja ap viņu.
Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
7 Tad Sauls sacīja uz saviem kalpiem, kas ap viņu stāvēja: klausiet jel, jūs Benjaminieši, vai Isajus dēls jums visiem dos tīrumus un vīna dārzus, vai viņš jūs visus cels par tūkstošniekiem un par simtniekiem, -
Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
8 Ka jūs visi pret mani esat sazvērējušies, un neviena nav, kas priekš manām ausīm būtu sacījis, ka mans dēls derību ir derējis ar Isajus dēlu? Un neviena nav jūsu starpā, kam manis būtu žēl, un kas to priekš manām ausīm būtu teicis, ka mans dēls manu kalpu pret mani pamodinājis, ka tas uz mani glūn, kā tas šodien redzams.
Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
9 Tad Doēgs, tas Edomietis, kas pie Saula kalpiem stāvēja, atbildēja un sacīja: es redzēju Isajus dēlu uz Nobu nākam pie Aķimeleka, Aķitaba dēla.
Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
10 Tas To Kungu viņa labad vaicāja un tam deva ceļamaizi un tam deva arī Fīlista Goliata zobenu.
Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
11 Tad ķēniņš nosūtīja un lika aicināt Aķimeleku, priestera Aķitaba dēlu, un visu viņa tēva namu, kas priesteri bija Nobā. Un tie nāca visi ķēniņa priekšā.
Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
12 Tad Sauls sacīja: klausi jel, tu Aķitaba dēls! Un tas sacīja: redzi, še es esmu, kungs.
Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
13 Tad Sauls uz to sacīja: kāpēc jūs pret mani esat sazvērējušies, tu un Isajus dēls, ka tu viņam esi maizes devis un zobenu, un Dievu viņa labad vaicājis, ka viņš pret mani celtos un uz mani glūnētu, kā tas šodien redzams?
Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
14 Tad Aķimeleks ķēniņam atbildēja un sacīja: kurš tad starp visiem taviem kalpiem ir tik uzticīgs, kā Dāvids, paša ķēniņa znots, kas pie tevis var pieiet un tevi klausīt un top godā turēts tavā namā?
Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
15 Vai tad es šodien esmu iesācis Dievu viņa pēc vaicāt? Lai Dievs pasargā! Lai ķēniņš tādu lietu uz savu kalpu negriež nedz uz visu mana tēva namu, jo tavs kalps no visām šīm lietām nekā nezin, ne mazu ne lielu.
A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
16 Bet ķēniņš sacīja: mirt tev jāmirst, Aķimelek, tev un visam tava tēva namam.
Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
17 Un ķēniņš sacīja uz tiem sargiem, kas pie viņa stāvēja: griežaties un nokaujiet Tā Kunga priesterus, tāpēc ka viņu roka arīdzan ir ar Dāvidu, un ka tie zinājuši viņu bēgam un man to nav sacījuši. Bet ķēniņa kalpi negribēja savu roku izstiept, Tā Kunga priesterus nokaut.
Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
18 Tad ķēniņš sacīja uz Doēgu: griezies tu un kauj tos priesterus. Tad Doēgs, tas Edomietis, griezās un kāva tos priesterus un nokāva tai diena astoņdesmit un piecus vīrus, kas to nātnu efodu nesa.
Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
19 Viņš sita arī Nobu, to priesteru pilsētu, ar zobena asmeni, gan vīrus, gan sievas, gan bērnus, gan zīdāmos, gan vēršus, gan ēzeļus, gan sīkus lopus viņš nokāva ar zobena asmeni.
Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
20 Tomēr viens no Aķimeleka, Aķitaba dēla, dēliem izbēga, ar vārdu Abjatars, un bēga pie Dāvida.
Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
21 Un Abjatars stāstīja Dāvidam, ka Sauls Tā Kunga priesterus bija nokāvis.
Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
22 Tad Dāvids sacīja uz Abjataru: es jau to zināju tai dienā, kad Doēgs, tas Edomietis, tur bija, ka tas Saulam to tiešām atsacīs. Es esmu noziedzīgs pie visām tava tēva nama dvēselēm.
Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
23 Paliec pie manis, nebīsties, kas manu dzīvību meklē, tam būs arī tavu dzīvību meklēt, jo pie manis tev būs patvērums.
Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”

< Pirmā Samuela 22 >