< Pirmā Ķēniņu 18 >

1 Un pēc ilga laika Tā Kunga vārds notika uz Eliju trešā gadā tā: ej, rādies Ahabam, un Es došu lietu zemes virsū.
Bayan dogon lokaci, a cikin shekara ta uku, maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce, “Tafi, ka gabatar da kanka ga Ahab, zan kuwa aika da ruwan sama a ƙasar.”
2 Un Elija nogāja, Ahabam rādīties, bet bads Samarijā bija grūts.
Saboda haka Iliya ya tafi ya gabatar da kansa ga Ahab. Yanzu dai yunwa ta tsananta a Samariya,
3 Un Ahabs bija aicinājis nama uzraugu Obadiju, un Obadija bijās To Kungu ļoti.
Ahab kuma ya aika a kawo Obadiya, sarkin fadansa (Obadiya dai cikakken mai gaskata da Ubangiji ne.
4 Jo kad Izebele bija izdeldējusi Tā Kunga praviešus, tad Obadija ņēma simts praviešus un tos apslēpa pa piecdesmit vienā alā un tos uzturēja ar maizi un ūdeni.
Yayinda Yezebel tana kisan annabawan Ubangiji, Obadiya ya ɗauki annabawa ɗari ya ɓoye a kogwanni biyu, hamsin a kowanne, ya kuma tanada musu abinci da kuma ruwa.)
5 Un Ahabs bija sacījis uz Obadiju: ej pa to zemi pie visiem ūdens avotiem un pie visām upēm, vai mēs neatradīsim zāli, ka dzīvus uzturam zirgus un zirgēzeļus, ka tie lopi visai neiet bojā.
Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka ratsa ƙasar zuwa dukan maɓulɓulai da fadamu. Mai yiwuwa ka sami ciyawa mu ba dawakai da alfadarai don su rayu, don kada mu kashe dabbobinmu.”
6 Un tie to zemi dalīja savā starpā, to parstaigāt; Ahabs gaja viens pa vienu ceļu, un Obadija gāja arīdzan viens pa otru ceļu.
Saboda haka suka raba ƙasar da za su ratsa, Ahab zai tafi gefe ɗaya, Obadiya kuma yă bi gefe ɗaya.
7 Kad nu Obadija bija ceļā, redzi, tad Elija tam nāca pretī, un viņš to pazīdams metās uz savu vaigu un sacīja: vai tu neesi mans kungs Elija?
Yayinda Obadiya yana tafiya, sai Iliya ya sadu da shi. Obadiya ya gane shi, ya rusuna har ƙasa, ya ce, “Kai ne, shugabana, Iliya?”
8 Un viņš sacīja: es tas esmu, ej, saki savam kungam: redzi, Elija ir še.
Iliya ya amsa, ya ce, “I, je ka faɗa wa maigidanka cewa, ‘Iliya yana a nan.’”
9 Bet viņš sacīja: ko es esmu grēkojis, ka tu savu kalpu dod Ahabam rokā, ka es topu nokauts?
Obadiya ya yi tambaya, “Me na yi da ba daidai ba, da kake miƙa bawanka ga Ahab don yă kashe?
10 Tik tiešām kā Tas Kungs, tavs Dievs, dzīvo, nav nevienas tautas, nedz valsts, kurp mans kungs nebūtu sūtījis, tevi meklēt. Un kad tie sacīja: še viņa nav, tad viņš tai valstij un tai tautai lika zvērēt, ka tie tevi nebija atraduši.
Na rantse da Ubangiji Allahnka, babu al’umma ko masarauta da mai girma sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka can, sai yă sa mulkin ko al’ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba.
11 Un nu tu saki: ej, saki savam kungam, redzi, Elija ir še.
Amma yanzu kana faɗa mini in tafi wurin mai girma in ce, ‘Iliya yana a nan.’
12 Un notiks, kad es no tevis aiziešu, un Tā Kunga gars tevi aizņems, kas zin kur, un ja es būtu gājis Ahabam to sacīt, un viņš tevi pēc neatrastu, tad viņš mani nokautu. Bet es tavs kalps bīstos To Kungu no savām jaunām dienām.
Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
13 Vai manam kungam nav sacīts, ko es esmu darījis, kad Izebele nokāva Tā Kunga praviešus, ka es simtu no Tā Kunga praviešiem apslēpu pa piecdesmit vienā alā un tos uzturēju ar maizi un ūdeni?
Ranka yă daɗe, ashe, ba a faɗa maka abin da na yi lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji ba? Yadda na ɓoye annabawa ɗari, na sa su hamsin-hamsin a kogwanni biyu, na yi ta ba su abinci da ruwa.
14 Un nu tu saki: ej, saki savam kungam, redzi, Elija ir še; tad jau viņš mani nokaus.
Yanzu fa, kana ce in tafi wurin mai girma sarki, in ce, ‘Iliya yana a nan.’ Ai, zai kashe ni!”
15 Tad Elija uz to sacīja: tik tiešām kā Tas Kungs Cebaot dzīvo, ka priekšā es stāvu, es šodien viņam rādīšos.
Iliya ya ce, “Na rantse da Ubangiji Maɗaukaki, wanda nake bauta wa, tabbatacce zan gabatar da kaina ga Ahab a yau.”
16 Tad Obadija nogāja Ahabam pretī un viņam to sacīja. Un Ahabs gāja Elijam pretī.
Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya.
17 Un kad Ahabs Eliju ieraudzīja, tad Ahabs uz to sacīja: vai tu tas esi, kas Israēli sajauc?
Sa’ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne wannan, kai mai tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila?”
18 Un viņš sacīja: es Israēli neesmu sajaucis, bet tu un tava tēva nams, caur to, ka jūs esat atstājuši Tā Kunga baušļus un Baāliem pakaļ staigājuši.
Iliya ya amsa, ya ce, “Ban tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila ba. Amma kai da iyalin mahaifinka, ku kuka tā-da-na-zaune-tsaye. Ka ƙyale umarnai Ubangiji, ka bi Ba’al.
19 Un nu sūti, sapulcini pie manis visu Israēli Karmeļa kalnā un tos četrsimt un piecdesmit Baāla praviešus un tos četrsimt Ašeras praviešus, kas ēd pie Izebeles galda.
Yanzu ka tara mutane daga dukan Isra’ila su sadu da ni a kan Dutsen Karmel. Ka kuma kawo annabawa ɗari huɗu da hamsin na Ba’al, da kuma annabawa ɗari huɗu na Ashera, waɗanda suke ci a teburin Yezebel.”
20 Tad Ahabs izsūtīja pie visiem Israēla bērniem un sapulcināja tos praviešus Karmeļa kalnā.
Sai Ahab ya aika a duk fāɗin Isra’ila, ya kuma tattara annabawan a kan Dutsen Karmel.
21 Tad Elija piegāja pie visiem ļaudīm un sacīja: cik ilgi jūs klibosiet uz abējām pusēm? Ja Tas Kungs ir Dievs, tad ejat viņam pakaļ, bet ja Baāls tas ir, tad ejat tam pakaļ. Un tie ļaudis tam neatbildēja ne vārda.
Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
22 Tad Elija sacīja uz tiem ļaudīm: es viens vienīgs esmu atlicis, Tā Kunga pravietis, bet Baāla praviešu ir četrsimt un piecdesmit.
Sai Iliya ya ce musu, “Ni ne kaɗai annabin Ubangiji da ya rage, amma Ba’al yana da annabawa ɗari huɗu da hamsin.
23 Un dodiet nu mums divus vēršus, un lai tie to vienu vērsi izvēlās un sacērt gabalos un liek uz malku, bet uguni tiem nebūs pielikt; tad es sataisīšu arī to otru vērsi un to likšu uz malku un nelikšu uguni klāt.
Ku samo mana bijimai biyu. Bari su zaɓa ɗaya wa kansu, bari kuma su yanka shi kucu-kucu su sa a itace, sai dai, kada su sa wuta a kansa. Ni kuwa zan shirya ɗaya bijimin in sa a kan itace, ni ma, ba zan sa wuta a kansa ba.
24 Tad piesauciet jūs sava dieva vārdu, bet es piesaukšu Tā Kunga vārdu: kurš Dievs nu ar uguni atbildēs, tas lai ir Dievs. Tad visi ļaudis atbildēja un sacīja: šis vārds ir labs.
Sa’an nan ku kira bisa sunan allahnku, ni kuwa zan kira bisa sunan Ubangiji. Duk allahn da ya amsa ta wurin wuta, shi ne Allah.” Sai dukan jama’a suka ce, “Abin nan da faɗa yana da kyau.”
25 Un Elija sacīja uz tiem Baāla praviešiem: izvēlaties to vienu vērsi un sataisiet to papriekš, jo jūs esat daudzi un piesauciet sava dieva vārdu, bet uguni neliekat klāt.
Iliya ya ce wa annabawan Ba’al, “Ku ku fara zaɓi bijimi ɗaya, ku shirya, da yake kuna da yawa. Ku kira a bisa sunan allahnku, amma kada ku ƙuna wuta.”
26 Tad tie ņēma to vērsi, ko viņš tiem deva un to sataisīja un piesauca Baāla vārdu no rīta līdz dienasvidum sacīdami: Baāl, paklausi mūs! Bet tur nebija ne balss, ne atbildes! Un tie lēkāja ap to altāri, kas bija taisīts.
Sai suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi. Sa’an nan suka kira bisa sunan Ba’al daga safe har tsakar rana. Suna ihu, “Ya Ba’al, ka amsa mana!” Amma babu wata amsa, babu wani da ya amsa. Suka yi ta rawa kewaye da bagaden da suka yi.
27 Un ap dienasvidu Elija tos apsmēja un sacīja: sauciet stiprā balsī, jo viņš taču ir dievs; viņš laikam ir domās vai darīšanās vai ceļā, varbūt ka viņš guļ, lai uzmostas.
Da tsakar rana, Iliya ya fara yin musu ba’a. Ya ce, “Ku yi ihu da ƙarfi, tabbatacce shi allah ne! Mai yiwuwa yana cikin zurfin tunani, ko dai aiki ya yi masa yawa, ko ya yi tafiya. Mai yiwuwa yana barci ne, dole a tashe shi.”
28 Un tie sauca ar stipru balsi un iegriezās pēc sava ieraduma ar nažiem un īleniem, kamēr tiem asinis tecēja.
Sai suka yi ta ihu da ƙarfi suna tsattsaga kansu da takuba da māsu, yadda al’adarsu take, sai da jininsu ya yi ta zuba.
29 Kad nu pusdiena jau bija pāri, tad tie vēl muldēja līdz ēdamā upura laikam; bet tur nebija ne balss, ne atbildes, ne uzklausīšanās.
Tsakar rana ta wuce, suka ci gaba da ƙoƙari, suna annabci har lokacin miƙa hadayar yamma ya yi. Amma babu wani da ya tanƙa, babu wani da ya amsa, babu wanda ya kula.
30 Tad Elija sacīja uz visiem ļaudīm: nāciet šurp pie manis. Tad visi ļaudis pie tā piegāja, un viņš uztaisīja atkal Tā Kunga altāri, kas bija salauzts.
Sa’an nan Iliya ya ce wa dukan mutane, “Ku zo nan wurina.” Suka zo wurinsa, ya kuma shirya bagaden Ubangiji, da ya riga ya zama kufai.
31 Un Elija ņēma divpadsmit akmeņus pēc Jēkaba bērnu skaita, uz ko Tā Kunga vārds bija noticis, sacīdams: tavu vārdu būs saukt Israēli.
Iliya ya ɗauki duwatsu goma sha biyu, ɗaya don kowace kabila zuriyar Yaƙub, wanda maganar Ubangiji ta zo masa, cewa, “Sunanka zai zama Isra’ila.”
32 Un viņš uztaisīja no tiem akmeņiem altāri Tā Kunga Vārdā, un taisīja bedri ap to altāri, tik platu, ka tur divi mēri labības varēja saiet.
Da waɗannan duwatsun ya gina bagade cikin sunan Ubangiji, ya kuma haƙa wuriya kewaye da shi, isashe da zai ci garwa biyu na irin ƙwayar gyada.
33 Un viņš salika malku un dalīja to vērsi gabalos un to nolika uz to malku.
Ya shirya itace, ya yayyanka bijimin kucu-kucu, ya shimfiɗa shi a itacen. Sa’an nan ya ce musu, “Ku cika manyan tuluna da ruwa, ku zuba a kan hadayar da kuma a kan itacen.” Suka zuba.
34 Un viņš sacīja: pildiet četrus traukus ar ūdeni un lejiet to uz to dedzināmo upuri un uz to malku. Un viņš sacīja: dariet to vēl otru reizi. Un tie to darīja otru reizi. Un viņš sacīja: dariet to trešo reizi, un tie to darīja trešo reizi.
Ya ce, “Ku sāke yin haka,” sai suka sāke yin haka. Ya umarta, “Ku yi haka sau na uku,” suka kuma yi haka sau na uku.
35 Un ūdens tecēja ap altāri, un bedre tapa pilna ar ūdeni.
Ruwan ya gangara kewaye da bagaden har ma ya cika wuriyar.
36 Un ap ēdamā upura laiku pravietis Elija piegāja un sacīja: Kungs, Ābrahāma, Īzaka un Israēla Dievs, šodien lai top zināms, ka Tu esi Dievs iekš Israēla un es Tavs kalps, un ka visu šo esmu darījis uz Tavu vārdu;
A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
37 Paklausi mani, Kungs, paklausi mani, lai šie ļaudis atzīst, ka Tu Kungs esi Dievs, un ka Tu viņu sirdi atgriezi atpakaļ.
Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, saboda waɗannan mutane su san cewa kai, ya Ubangiji, kai ne Allah, su kuma san cewa kana sāke juye zukatansu zuwa gare ka.”
38 Tad Tā Kunga uguns krita zemē un aprija to dedzināmo upuri un to malku un tos akmeņus un to zemi un uzlaizīja arī to ūdeni bedrē.
Sai wutar Ubangiji ya fāɗo, ya cinye hadayar, itacen, duwatsun da kuma ƙasar, ya lashe ruwan da yake cikin wuriyar.
39 Kad nu visi ļaudis to redzēja, tad tie metās uz savu vaigu un sacīja: Tas Kungs ir Dievs, Tas Kungs ir Dievs.
Sa’ad da mutane suka ga wannan, sai suka rusuna, suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji, shi ne Allah! Ubangiji, shi ne Allah!”
40 Un Elija uz tiem sacīja: grābiet Baāla praviešus, ka neviens no tiem neizsprūk! Tad tie tos sagrāba. Un Elija tos noveda pie Ķizones upes un tos tur nokāva.
Sa’an nan Iliya ya umarce su, ya ce, “Ku kama annabawan Ba’al, kada ku bar waninsu yă tsere!” Suka kama su, Iliya kuwa ya sa aka gangara da su zuwa Kwarin Kishon, aka yayyanka su a can.
41 Tad Elija sacīja uz Ahabu: celies, ēd un dzer, jo šņāc kā uz lietu.
Sai Iliya ya ce wa Ahab, “Ka haura gida, ka ci, ka sha, gama ina jin motsin ruwan sama mai yawa.”
42 Un Ahabs gāja ēst un dzert, bet Elija gāja Karmeļa kalna galā un metās zemē un lika savu vaigu starp saviem ceļiem.
Sai Ahab ya ruga don yă ci, yă sha, amma Iliya ya hau kan ƙwanƙolin Karmel, ya rusuna ƙasa, ya sa fuska a tsakanin gwiwarsa.
43 Un viņš sacīja uz savu puisi: ej jel un skaties uz jūru. Tad tas gāja un skatījās un sacīja: tur nav nekā. Tad viņš sacīja: ej atkal! Septiņām lāgām.
Ya ce wa bawansa, “Tafi ka dubi wajen teku.” Sai bawan ya haura ya duba. Ya ce, “Ba kome a can.” Sau bakwai Iliya ya ce, “Koma.”
44 Un septītā reizē viņš sacīja: redzi, mazs mākonīts, kā vīra plauksta, ceļas no jūras. Tad viņš sacīja: noej, saki Ahabam jūdz un brauc, ka lietus tevi neaizņem.
Sau na bakwai, bawan ya ce, “Wani girgije ƙarami kamar hannun mutum yana tasowa daga teku.” Sai Iliya ya ce, “Je ka faɗa wa Ahab, ‘Shirya keken yaƙinka, ka gangara kafin ruwan sama yă tare ka.’”
45 Un pēc tam debess apmācās ar melniem mākoņiem un vētru un stiprs lietus gāzās. Un Ahabs sēdās ratos un brauca uz Jezreēli.
Ana cikin haka, sarari ya ƙara duhunta da girgije, iska ta taso, sai ruwan sama kamar da bakin kwarya ya sauko, Ahab kuwa ya hau zuwa Yezireyel.
46 Un Tā Kunga roka nāca pār Eliju, un tas apjoza savus gurnus un skrēja Ahabam pa priekšu līdz Jezreēlei.
Ikon Ubangiji ya sauko a kan Iliya, ya sha ɗamara, ya ruga a guje a gaban Ahab har zuwa Yezireyel.

< Pirmā Ķēniņu 18 >