< Pirmā Ķēniņu 14 >

1 Tanī laikā Abija, Jerobeama dēls, saslima.
A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
2 Un Jerobeams sacīja uz savu sievu: celies un pārģērbies, ka neviens tevi nepazīst, ka tu esi Jerobeama sieva, un ej uz Šīlo; redzi, tur ir pravietis Ahija, kas par mani runājis, ka es būšot ķēniņš pār šiem ļaudīm.
sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
3 Un ņem savā rokā desmit maizes un raušus un krūzi ar medu, un ej pie viņa; viņš tev dos ziņu, kas tam bērnam notiks.
Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
4 Un Jerobeama sieva tā darīja un cēlās un gāja uz Šīlo un nāca Ahijas namā. Bet Ahija nevarēja redzēt, jo viņa acis bija tumšas metušās no vecuma.
Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
5 Bet Tas Kungs sacīja uz Ahiju: redzi, Jerobeama sieva nāk, tev ko vaicāt sava dēla pēc, jo tas ir slims. Tā un tā tev uz viņu būs runāt; kad viņa nāks, tad izliksies sveša.
Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
6 Kad nu Ahija dzirdēja viņas kāju troksni, viņai pa durvīm ienākot, tad viņš sacīja: nāc iekšā, Jerobeama sieva, kāpēc tu liecies sveša? Es tev esmu bargs vēstnesis.
Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
7 Ej, saki Jerobeamam: tā saka Tas Kungs, Israēla Dievs: tāpēc ka Es tevi paaugstinājis no tiem ļaudīm un tevi par valdītāju cēlis pār Maniem Israēla ļaudīm,
Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
8 Un atrāvis valstību no Dāvida nama un tev to devis, un tu neesi bijis kā Mans kalps Dāvids, kas Manus baušļus sargājis un pie Manis turējies ar visu savu sirdi, darīdams vien, kas pareizi Manās acīs;
Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
9 Bet tu esi ļaunu darījis vairāk nekā visi, kas priekš tevis bijuši, un nogājis un sev citus dievus taisījis un lietas bildes taisījis, Mani kaitināt, un tu Mani esi atmetis:
Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
10 Tāpēc redzi, Es vedīšu ļaunumu pār Jerobeama namu un izdeldēšu no Jerobeama visu, kas mīž pie sienas, tos lielos un tos mazos iekš Israēla, un izmēzīšu Jerobeama nama pēcnākamus, itin kā sūdi top izmēzti, tiekams tas visai būs pagalam.
“‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
11 Kas no Jerobeama mirst pilsētā, to suņi ēdīs, un kas mirst laukā, to putni apakš debess ēdīs, jo Tas Kungs to runājis.
Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
12 Bet tu, celies, ej uz mājām, un kad tavas kājas ieies pilsēta, tad tas bērns mirs.
“Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
13 Un viss Israēls viņu nožēlos un viņu apraks, jo šis vien no Jerobeama nāks kapā, tāpēc ka Tas Kungs, Israēla Dievs, iekš tā ko laba atradis Jerobeama namā.
Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
14 Bet Tas Kungs sev iecels ķēniņu pār Israēli, kas Jerobeama namu tai dienā izdeldēs. Un ko? Tas jau ir klātu.
“Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
15 Tas Kungs sitīs Israēli, itin kā niedre ūdenī top šaubīta, un izstums Israēli no šās labās zemes, ko Viņš devis viņu tēviem, un tos izkaisīs viņpus upes, tāpēc ka tie sev elkastabus taisījuši, To Kungu kaitinādami.
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
16 Un Viņš Israēli nodos Jerobeama grēku dēļ, ar ko pats grēkojis un Israēli apgrēcinājis.
Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
17 Tad Jerobeama sieva cēlās un gāja un nonāca Tircā. Kad nu viņa pie nama sliekšņa nāca, tad tas bērns nomira.
Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
18 Un to apraka, un viss Israēls viņu apgauda pēc Tā Kunga vārda, ko Viņš bija runājis caur Savu kalpu, pravieti Ahiju.
Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
19 Un kas vēl par Jerobeamu stāstāms, kā tas karojis un kā tas valdījis, redzi, tas rakstīts Israēla ķēniņu laiku grāmatā.
Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
20 Un tas laiks, kamēr Jerobeams ķēniņš bijis, ir divdesmit un divi gadi; un tas aizmiga saviem tēviem pakaļ; un viņa dēls Nadabs palika par ķēniņu viņa vietā.
Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Un Rekabeams, Salamana dēls, bija ķēniņš pār Jūdu. Četrdesmit un vienu gadu Rekabeams bija vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja septiņpadsmit gadus Jeruzālemes pilsētā, ko Tas Kungs no visām Israēla ciltīm bija izredzējis, tur likt savu vārdu. Un viņa mātes vārds bija Naēma, Amoniete.
Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
22 Un Jūda darīja, kas Tam Kungam nepatika, un tie viņu vairāk apkaitināja, nekā visi viņu tēvi bija darījuši ar saviem grēkiem, ar ko tie bija grēkojuši.
Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
23 Un tie arīdzan taisīja sev kalnu altārus un elku bildes un elku stabus uz ikkatra augsta kalna un apakš visiem zaļiem kokiem.
Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
24 Un maucinieki bija tai zemē un darīja pēc visām pagānu negantībām, ko Tas Kungs bija izdzinis Israēla bērnu priekšā.
Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
25 Un ķēniņa Rekabeama piektā gadā Zizaks, Ēģiptes ķēniņš, cēlās pret Jeruzālemi,
A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
26 Un paņēma Tā Kunga nama mantas un ķēniņa nama mantas: viņš paņēma visu, ir visas priekšturamās zelta bruņas viņš paņēma, ko Salamans bija licis taisīt.
Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
27 Ķēniņš Rekabeams viņu vietā taisīja priekšturamās bruņas no vara, un tās deva pils karavīru virsnieku rokā, kas apsargāja ķēniņa nama durvis.
Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
28 Kad nu ķēniņš uz Tā Kunga namu gāja, tad pils karavīri tās nesa un pēc tie tās atkal nonesa pils karavīru istabā.
Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
29 Kas vēl stāstāms par Rekabeamu un par visu, ko viņš darījis, redzi, tas rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
30 Un starp Rekabeamu un Jerobeamu bija karš visu mūžu.
Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
31 Un Rekabeams gāja dusēt pie saviem tēviem un tapa aprakts pie saviem tēviem Dāvida pilsētā. Un viņa mātes vārds bija Naēma, Amoniete, un viņa dēls Abijams palika par ķēniņu viņa vietā.
Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< Pirmā Ķēniņu 14 >