< Psalmorum 92 >

1 psalmus cantici in die sabbati bonum est confiteri Domino et psallere nomini tuo Altissime
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 ad adnuntiandum mane misericordiam tuam et veritatem tuam per noctem
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 in decacordo psalterio cum cantico in cithara
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 quia delectasti me Domine in factura tua et in operibus manuum tuarum exultabo
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 quam magnificata sunt opera tua Domine nimis profundae factae sunt cogitationes tuae
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 vir insipiens non cognoscet et stultus non intelleget haec
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 cum exorti fuerint peccatores sicut faenum et apparuerint omnes qui operantur iniquitatem ut intereant in saeculum saeculi
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 tu autem Altissimus in aeternum Domine
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 quoniam ecce inimici tui Domine; quoniam ecce inimici tui peribunt et dispergentur omnes qui operantur iniquitatem
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 et exaltabitur sicut unicornis cornu meum et senectus mea in misericordia uberi
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 et despexit oculus meus inimicis meis et insurgentibus in me malignantibus audiet auris mea
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 iustus ut palma florebit ut cedrus Libani multiplicabitur
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 plantati in domo Domini in atriis Dei nostri florebunt
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 adhuc multiplicabuntur in senecta uberi et bene patientes erunt
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 ut adnuntient quoniam rectus Dominus Deus noster et non est iniquitas in eo
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Psalmorum 92 >