< Psalmorum 88 >
1 canticum psalmi filiis Core in finem pro Maeleth ad respondendum intellectus Eman Ezraitae Domine Deus salutis meae die clamavi et nocte coram te
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 intret in conspectu tuo oratio mea inclina aurem tuam ad precem meam
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 quia repleta est malis anima mea et vita mea in inferno adpropinquavit (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 aestimatus sum cum descendentibus in lacum factus sum sicut homo sine adiutorio
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 inter mortuos liber sicut vulnerati dormientes in sepulchris quorum non es memor amplius et ipsi de manu tua repulsi sunt
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 posuerunt me in lacu inferiori in tenebrosis et in umbra mortis
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 super me confirmatus est furor tuus et omnes fluctus tuos induxisti super me diapsalma
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 longe fecisti notos meos a me posuerunt me abominationem sibi traditus sum et non egrediebar
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 oculi mei languerunt prae inopia clamavi ad te Domine tota die expandi ad te manus meas
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 numquid mortuis facies mirabilia aut medici suscitabunt et confitebuntur tibi diapsalma
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 numquid narrabit aliquis in sepulchro misericordiam tuam et veritatem tuam in perditione
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 numquid cognoscentur in tenebris mirabilia tua et iustitia tua in terra oblivionis
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 et ego ad te Domine clamavi et mane oratio mea praeveniet te
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 ut quid Domine repellis orationem meam avertis faciem tuam a me
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 pauper sum ego et in laboribus a iuventute mea exaltatus autem humiliatus sum et conturbatus
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 in me transierunt irae tuae et terrores tui conturbaverunt me
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 circuierunt me sicut aqua tota die circumdederunt me simul
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 elongasti a me amicum et proximum et notos meos a miseria
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.