< Psalmorum 81 >

1 in finem pro torcularibus Asaph exultate Deo adiutori nostro iubilate Deo Iacob
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 sumite psalmum et date tympanum psalterium iucundum cum cithara
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 bucinate in neomenia tuba in insigni die sollemnitatis nostrae
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 quia praeceptum Israhel est et iudicium Dei Iacob
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 testimonium in Ioseph posuit illud cum exiret de terra Aegypti linguam quam non noverat audivit
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 devertit ab oneribus dorsum eius manus eius in cofino servierunt
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 in tribulatione invocasti me et liberavi te exaudivi te in abscondito tempestatis probavi te apud aquam Contradictionis diapsalma
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 audi populus meus et contestabor te Israhel si audias me
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 non erit in te deus recens nec adorabis deum alienum
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 ego enim sum Dominus Deus tuus qui eduxi te de terra Aegypti dilata os tuum et implebo illud
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 et non audivit populus meus vocem meam et Israhel non intendit mihi
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 et dimisi illos secundum desideria cordis eorum ibunt in adinventionibus suis
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 si populus meus audisset me Israhel si in viis meis ambulasset
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 pro nihilo forsitan inimicos eorum humiliassem et super tribulantes eos misissem manum meam
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 inimici Domini mentiti sunt ei et erit tempus eorum in saeculo
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 et cibavit illos ex adipe frumenti et de petra melle saturavit illos
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Psalmorum 81 >