< Psalmorum 72 >

1 in Salomonem
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Deus iudicium tuum regi da et iustitiam tuam filio regis iudicare populum tuum in iustitia et pauperes tuos in iudicio
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 suscipiant montes pacem populo et colles iustitiam
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 iudicabit pauperes populi et salvos faciet filios pauperum et humiliabit calumniatorem
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 et permanebit cum sole et ante lunam generationes generationum
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 descendet sicut pluvia in vellus et sicut stillicidia stillantia super terram
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 orietur in diebus eius iustitia et abundantia pacis donec auferatur luna
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 et dominabitur a mari usque ad mare et a flumine usque ad terminos orbis terrarum
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 coram illo procident Aethiopes et inimici eius terram lingent
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 reges Tharsis et insulae munera offerent reges Arabum et Saba dona adducent
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 et adorabunt eum omnes reges omnes gentes servient ei
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 quia liberavit pauperem a potente et pauperem cui non erat adiutor
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 parcet pauperi et inopi et animas pauperum salvas faciet
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 ex usuris et iniquitate redimet animas eorum et honorabile nomen eorum coram illo
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 et vivet et dabitur ei de auro Arabiae et orabunt de ipso semper tota die benedicent ei
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 erit firmamentum in terra in summis montium superextolletur super Libanum fructus eius et florebunt de civitate sicut faenum terrae
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 sit nomen eius benedictum in saecula ante solem permanet nomen eius et benedicentur in ipso omnes tribus terrae omnes gentes beatificabunt eum
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 benedictus Dominus Deus Deus Israhel qui facit mirabilia solus
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 et benedictum nomen maiestatis eius in aeternum et replebitur maiestate eius omnis terra fiat fiat
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 defecerunt laudes David filii Iesse
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Psalmorum 72 >