< Psalmorum 69 >

1 in finem pro his qui commutabuntur David salvum me fac Deus quoniam intraverunt aquae usque ad animam meam
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 infixus sum in limum profundi et non est substantia veni in altitudines maris et tempestas demersit me
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 laboravi clamans raucae factae sunt fauces meae defecerunt oculi mei dum spero in Deum meum
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 multiplicati sunt super capillos capitis mei qui oderunt me gratis confortati sunt qui persecuti sunt me inimici mei iniuste quae non rapui tunc exsolvebam
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 Deus tu scis insipientiam meam et delicta mea a te non sunt abscondita
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 non erubescant in me qui expectant te Domine Domine virtutum non confundantur super me qui quaerunt te Deus Israhel
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 quoniam propter te sustinui obprobrium operuit confusio faciem meam
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 extraneus factus sum fratribus meis et peregrinus filiis matris meae
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 quoniam zelus domus tuae comedit me et obprobria exprobrantium tibi ceciderunt super me
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 et operui in ieiunio animam meam et factum est in obprobrium mihi
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 et posui vestimentum meum cilicium et factus sum illis in parabolam
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 adversum me exercebantur qui sedebant in porta et in me psallebant qui bibebant vinum
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 ego vero orationem meam ad te Domine tempus beneplaciti Deus in multitudine misericordiae tuae exaudi me in veritate salutis tuae
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 eripe me de luto ut non infigar liberer ab his qui oderunt me et de profundis aquarum
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 non me demergat tempestas aquae neque absorbeat me profundum neque urgeat super me puteus os suum
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 exaudi me Domine quoniam benigna est misericordia tua secundum multitudinem miserationum tuarum respice me
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 et ne avertas faciem tuam a puero tuo quoniam tribulor velociter exaudi me
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 intende animae meae et libera eam propter inimicos meos eripe me
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 tu scis inproperium meum et confusionem et reverentiam meam
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 in conspectu tuo sunt omnes qui tribulant me inproperium expectavit cor meum et miseriam et sustinui qui simul contristaretur et non fuit et qui consolaretur et non inveni
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 et dederunt in escam meam fel et in siti mea potaverunt me aceto
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 fiat mensa eorum coram ipsis in laqueum et in retributiones et in scandalum
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 obscurentur oculi eorum ne videant et dorsum eorum semper incurva
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 effunde super eos iram tuam et furor irae tuae conprehendat eos
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 fiat habitatio eorum deserta et in tabernaculis eorum non sit qui inhabitet
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 quoniam quem tu percussisti persecuti sunt et super dolorem vulnerum meorum addiderunt
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 adpone iniquitatem super iniquitatem eorum et non intrent in iustitia tua
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 deleantur de libro viventium et cum iustis non scribantur
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 ego sum pauper et dolens salus tua Deus suscepit me
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 laudabo nomen Dei cum cantico magnificabo eum in laude
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 et placebit Deo super vitulum novellum cornua producentem et ungulas
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 videant pauperes et laetentur quaerite Deum et vivet anima vestra
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 quoniam exaudivit pauperes Dominus et vinctos suos non despexit
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 laudent illum caeli et terra mare et omnia reptilia in eis
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 quoniam Deus salvam faciet Sion et aedificabuntur civitates Iudaeae et inhabitabunt ibi et hereditate adquirent eam
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 et semen servorum eius possidebunt eam et qui diligunt nomen eius habitabunt in ea
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Psalmorum 69 >