< Psalmorum 62 >

1 in finem pro Idithun psalmus David nonne Deo subiecta erit anima mea ab ipso enim salutare meum
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 nam et ipse Deus meus et salutaris meus susceptor meus non movebor amplius
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 quousque inruitis in hominem interficitis universi vos tamquam parieti inclinato et maceriae depulsae
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 verumtamen pretium meum cogitaverunt repellere cucurri in siti ore suo benedicebant et corde suo maledicebant diapsalma
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 verumtamen Deo subiecta esto anima mea quoniam ab ipso patientia mea
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 quia ipse Deus meus et salvator meus adiutor meus non emigrabo
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 in Deo salutare meum et gloria mea Deus auxilii mei et spes mea in Deo est
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 sperate in eo omnis congregatio populi effundite coram illo corda vestra Deus adiutor noster in aeternum
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 verumtamen vani filii hominum mendaces filii hominum in stateris ut decipiant ipsi de vanitate in id ipsum
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 nolite sperare in iniquitate et rapinas nolite concupiscere divitiae si affluant nolite cor adponere
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 semel locutus est Deus duo haec audivi quia potestas Dei
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 et tibi Domine misericordia quia tu reddes unicuique iuxta opera sua
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”

< Psalmorum 62 >