< Psalmorum 38 >

1 psalmus David in rememorationem de sabbato Domine ne in furore tuo arguas me neque in ira tua corripias me
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 quoniam sagittae tuae infixae sunt mihi et confirmasti super me manum tuam
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 non est sanitas carni meae a facie irae tuae non est pax ossibus meis a facie peccatorum meorum
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 quoniam iniquitates meae supergressae sunt caput meum sicut onus grave gravatae sunt super me
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 putruerunt et corruptae sunt cicatrices meae a facie insipientiae meae
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 miser factus sum et curvatus sum usque ad finem tota die contristatus ingrediebar
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 quoniam lumbi mei impleti sunt inlusionibus et non est sanitas in carne mea
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 adflictus sum et humiliatus sum nimis rugiebam a gemitu cordis mei
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 Domine ante te omne desiderium meum et gemitus meus a te non est absconditus
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 cor meum conturbatum est dereliquit me virtus mea et lumen oculorum meorum et ipsum non est mecum
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 amici mei et proximi mei adversus me adpropinquaverunt et steterunt et qui iuxta me erant de longe steterunt
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 et vim faciebant qui quaerebant animam meam et qui inquirebant mala mihi locuti sunt vanitates et dolos tota die meditabantur
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 ego autem tamquam surdus non audiebam et sicut mutus non aperiens os suum
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 et factus sum sicut homo non audiens et non habens in ore suo redargutiones
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 quoniam in te Domine speravi tu exaudies Domine Deus meus
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 quia dixi nequando supergaudeant mihi inimici mei et dum commoventur pedes mei super me magna locuti sunt
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 quoniam ego in flagella paratus et dolor meus in conspectu meo semper
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 quoniam iniquitatem meam adnuntiabo et cogitabo pro peccato meo
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 inimici autem mei vivent et firmati sunt super me et multiplicati sunt qui oderunt me inique
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 qui retribuunt mala pro bonis detrahebant mihi quoniam sequebar bonitatem
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 non derelinquas me Domine Deus meus ne discesseris a me
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
22 intende in adiutorium meum Domine salutis meae
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.

< Psalmorum 38 >