< Psalmorum 135 >

1 alleluia laudate nomen Domini laudate servi Dominum
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 qui statis in domo Domini in atriis domus Dei nostri
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 laudate Dominum quia bonus Dominus psallite nomini eius quoniam suave
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 quoniam Iacob elegit sibi Dominus Israhel in possessionem sibi
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 quia ego cognovi quod magnus est Dominus et Deus noster prae omnibus diis
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 omnia quae voluit Dominus fecit in caelo et in terra in mare et in omnibus abyssis
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 educens nubes ab extremo terrae fulgora in pluviam fecit qui producit ventos de thesauris suis
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 qui percussit primogenita Aegypti ab homine usque ad pecus
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 emisit signa et prodigia in medio tui Aegypte in Pharaonem et in omnes servos eius
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 qui percussit gentes multas et occidit reges fortes
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Seon regem Amorreorum et Og regem Basan et omnia regna Chanaan
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 et dedit terram eorum hereditatem hereditatem Israhel populo suo
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Domine nomen tuum in aeternum Domine memoriale tuum in generationem et generationem
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 quia iudicabit Dominus populum suum et in servis suis deprecabitur
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 simulacra gentium argentum et aurum opera manuum hominum
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 os habent et non loquentur oculos habent et non videbunt
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 aures habent et non audient neque enim est spiritus in ore eorum
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 similes illis fiant qui faciunt ea et omnes qui sperant in eis
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 domus Israhel benedicite Domino domus Aaron benedicite Domino
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 domus Levi benedicite Domino qui timetis Dominum benedicite Domino
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 benedictus Dominus ex Sion qui habitat in Hierusalem
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalmorum 135 >