< Psalmorum 130 >

1 canticum graduum de profundis clamavi ad te Domine
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Domine exaudi vocem meam fiant aures tuae intendentes in vocem deprecationis meae
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 si iniquitates observabis Domine Domine quis sustinebit
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 quia apud te propitiatio est propter legem tuam sustinui te Domine sustinuit anima mea in verbum eius
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 speravit anima mea in Domino
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 a custodia matutina usque ad noctem speret Israhel in Domino
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 quia apud Dominum misericordia et copiosa apud eum redemptio
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 et ipse redimet Israhel ex omnibus iniquitatibus eius
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psalmorum 130 >