< Proverbiorum 8 >

1 numquid non sapientia clamitat et prudentia dat vocem suam
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 in summis excelsisque verticibus super viam in mediis semitis stans
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 iuxta portas civitatis in ipsis foribus loquitur dicens
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 o viri ad vos clamito et vox mea ad filios hominum
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 intellegite parvuli astutiam et insipientes animadvertite
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 audite quoniam de rebus magnis locutura sum et aperientur labia mea ut recta praedicent
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 veritatem meditabitur guttur meum et labia mea detestabuntur impium
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 iusti sunt omnes sermones mei non est in eis pravum quid neque perversum
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 recti sunt intellegentibus et aequi invenientibus scientiam
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 accipite disciplinam meam et non pecuniam doctrinam magis quam aurum eligite
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 melior est enim sapientia cunctis pretiosissimis et omne desiderabile ei non potest conparari
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 ego sapientia habito in consilio et eruditis intersum cogitationibus
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 timor Domini odit malum arrogantiam et superbiam et viam pravam et os bilingue detestor
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 meum est consilium et aequitas mea prudentia mea est fortitudo
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 per me reges regnant et legum conditores iusta decernunt
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 per me principes imperant et potentes decernunt iustitiam
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 ego diligentes me diligo et qui mane vigilant ad me invenient me
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 mecum sunt divitiae et gloria opes superbae et iustitia
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 melior est fructus meus auro et pretioso lapide et genimina mea argento electo
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 in viis iustitiae ambulo in medio semitarum iudicii
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 ut ditem diligentes me et thesauros eorum repleam
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 Dominus possedit me initium viarum suarum antequam quicquam faceret a principio
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 ab aeterno ordita sum et ex antiquis antequam terra fieret
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 necdum erant abyssi et ego iam concepta eram necdum fontes aquarum eruperant
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 necdum montes gravi mole constiterant ante colles ego parturiebar
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 adhuc terram non fecerat et flumina et cardines orbis terrae
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 quando praeparabat caelos aderam quando certa lege et gyro vallabat abyssos
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 quando aethera firmabat sursum et librabat fontes aquarum
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 quando circumdabat mari terminum suum et legem ponebat aquis ne transirent fines suos quando adpendebat fundamenta terrae
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 cum eo eram cuncta conponens et delectabar per singulos dies ludens coram eo omni tempore
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 ludens in orbe terrarum et deliciae meae esse cum filiis hominum
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 nunc ergo filii audite me beati qui custodiunt vias meas
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 audite disciplinam et estote sapientes et nolite abicere eam
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 beatus homo qui audit me qui vigilat ad fores meas cotidie et observat ad postes ostii mei
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 qui me invenerit inveniet vitam et hauriet salutem a Domino
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 qui autem in me peccaverit laedet animam suam omnes qui me oderunt diligunt mortem
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Proverbiorum 8 >