< Liber Numeri 34 >

1 locutus est Dominus ad Mosen
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 praecipe filiis Israhel et dices ad eos cum ingressi fueritis terram Chanaan et in possessionem vobis sorte ceciderit his finibus terminabitur
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 pars meridiana incipiet a solitudine Sin quae est iuxta Edom et habebit terminos contra orientem mare Salsissimum
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 qui circumibunt australem plagam per ascensum Scorpionis ita ut transeant Senna et perveniant in meridiem usque ad Cadesbarne unde egredientur confinia ad villam nomine Addar et tendent usque Asemona
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 ibitque per gyrum terminus ab Asemona usque ad torrentem Aegypti et maris Magni litore finietur
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 plaga autem occidentalis a mari Magno incipiet et ipso fine cludetur
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 porro ad septentrionalem plagam a mari Magno termini incipient pervenientes usque ad montem Altissimum
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 a quo venies in Emath usque ad terminos Sedada
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 ibuntque confinia usque Zephrona et villam Henan hii erunt termini in parte aquilonis
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 inde metabuntur fines contra orientalem plagam de villa Henan usque Sephama
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 et de Sephama descendent termini in Rebla contra fontem inde pervenient contra orientem ad mare Chenereth
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 et tendent usque Iordanem et ad ultimum Salsissimo cludentur mari hanc habebitis terram per fines suos in circuitu
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 praecepitque Moses filiis Israhel dicens haec erit terra quam possidebitis sorte et quam iussit dari Dominus novem tribubus et dimidiae tribui
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 tribus enim filiorum Ruben per familias suas et tribus filiorum Gad iuxta cognationum numerum media quoque tribus Manasse
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 id est duae semis tribus acceperunt partem suam trans Iordanem contra Hiericho ad orientalem plagam
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 et ait Dominus ad Mosen
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 haec sunt nomina virorum qui terram vobis divident Eleazar sacerdos et Iosue filius Nun
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 et singuli principes de tribubus singulis
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 quorum ista sunt vocabula de tribu Iuda Chaleb filius Iepphonne
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 de tribu Symeon Samuhel filius Ammiud
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 de tribu Beniamin Helidad filius Chaselon
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 de tribu filiorum Dan Bocci filius Iogli
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 filiorum Ioseph de tribu Manasse Hannihel filius Ephod
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 de tribu Ephraim Camuhel filius Sephtan
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 de tribu Zabulon Elisaphan filius Pharnach
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 de tribu Isachar dux Faltihel filius Ozan
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 de tribu Aser Ahiud filius Salomi
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 de tribu Nepthali Phedahel filius Ameiud
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 hii sunt quibus praecepit Dominus ut dividerent filiis Israhel terram Chanaan
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.

< Liber Numeri 34 >