< Liber Numeri 17 >

1 et locutus est Dominus ad Mosen dicens
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 loquere ad filios Israhel et accipe ab eis virgas singulas per cognationes suas a cunctis principibus tribuum virgas duodecim et uniuscuiusque nomen superscribes virgae suae
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
3 nomen autem Aaron erit in tribu Levi et una virga cunctas eorum familias continebit
A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
4 ponesque eas in tabernaculo foederis coram testimonio ubi loquar ad te
Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
5 quem ex his elegero germinabit virga eius et cohibebo a me querimonias filiorum Israhel quibus contra vos murmurant
Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
6 locutusque est Moses ad filios Israhel et dederunt ei omnes principes virgas per singulas tribus fueruntque virgae duodecim absque virga Aaron
Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
7 quas cum posuisset Moses coram Domino in tabernaculo testimonii
Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
8 sequenti die regressus invenit germinasse virgam Aaron in domo Levi et turgentibus gemmis eruperant flores qui foliis dilatatis in amigdalas deformati sunt
Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
9 protulit ergo Moses omnes virgas de conspectu Domini ad cunctos filios Israhel videruntque et receperunt singuli virgas suas
Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
10 dixitque Dominus ad Mosen refer virgam Aaron in tabernaculum testimonii ut servetur ibi in signum rebellium filiorum et quiescant querellae eorum a me ne moriantur
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
11 fecitque Moses sicut praeceperat Dominus
Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
12 dixerunt autem filii Israhel ad Mosen ecce consumpti sumus omnes perivimus
Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
13 quicumque accedit ad tabernaculum Domini moritur num usque ad internicionem cuncti delendi sumus
Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”

< Liber Numeri 17 >