< Mattheum 24 >
1 et egressus Iesus de templo ibat et accesserunt discipuli eius ut ostenderent ei aedificationes templi
Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
2 ipse autem respondens dixit eis videtis haec omnia amen dico vobis non relinquetur hic lapis super lapidem qui non destruatur
Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
3 sedente autem eo super montem Oliveti accesserunt ad eum discipuli secreto dicentes dic nobis quando haec erunt et quod signum adventus tui et consummationis saeculi (aiōn )
Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
4 et respondens Iesus dixit eis videte ne quis vos seducat
Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
5 multi enim venient in nomine meo dicentes ego sum Christus et multos seducent
Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
6 audituri autem estis proelia et opiniones proeliorum videte ne turbemini oportet enim haec fieri sed nondum est finis
Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
7 consurget enim gens in gentem et regnum in regnum et erunt pestilentiae et fames et terraemotus per loca
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
8 haec autem omnia initia sunt dolorum
Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
9 tunc tradent vos in tribulationem et occident vos et eritis odio omnibus gentibus propter nomen meum
“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
10 et tunc scandalizabuntur multi et invicem tradent et odio habebunt invicem
A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
11 et multi pseudoprophetae surgent et seducent multos
annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
12 et quoniam abundabit iniquitas refrigescet caritas multorum
Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
13 qui autem permanserit usque in finem hic salvus erit
amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 et praedicabitur hoc evangelium regni in universo orbe in testimonium omnibus gentibus et tunc veniet consummatio
Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
15 cum ergo videritis abominationem desolationis quae dicta est a Danihelo propheta stantem in loco sancto qui legit intellegat
“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
16 tunc qui in Iudaea sunt fugiant ad montes
to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
17 et qui in tecto non descendat tollere aliquid de domo sua
Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
18 et qui in agro non revertatur tollere tunicam suam
Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
19 vae autem praegnatibus et nutrientibus in illis diebus
Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
20 orate autem ut non fiat fuga vestra hieme vel sabbato
Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
21 erit enim tunc tribulatio magna qualis non fuit ab initio mundi usque modo neque fiet
Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
22 et nisi breviati fuissent dies illi non fieret salva omnis caro sed propter electos breviabuntur dies illi
“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
23 tunc si quis vobis dixerit ecce hic Christus aut illic nolite credere
A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
24 surgent enim pseudochristi et pseudoprophetae et dabunt signa magna et prodigia ita ut in errorem inducantur si fieri potest etiam electi
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
26 si ergo dixerint vobis ecce in deserto est nolite exire ecce in penetrabilibus nolite credere
“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
27 sicut enim fulgur exit ab oriente et paret usque in occidente ita erit et adventus Filii hominis
Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
28 ubicumque fuerit corpus illuc congregabuntur aquilae
Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
29 statim autem post tribulationem dierum illorum sol obscurabitur et luna non dabit lumen suum et stellae cadent de caelo et virtutes caelorum commovebuntur
“Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
30 et tunc parebit signum Filii hominis in caelo et tunc plangent omnes tribus terrae et videbunt Filium hominis venientem in nubibus caeli cum virtute multa et maiestate
“A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
31 et mittet angelos suos cum tuba et voce magna et congregabunt electos eius a quattuor ventis a summis caelorum usque ad terminos eorum
Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
32 ab arbore autem fici discite parabolam cum iam ramus eius tener fuerit et folia nata scitis quia prope est aestas
“Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
33 ita et vos cum videritis haec omnia scitote quia prope est in ianuis
Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
34 amen dico vobis quia non praeteribit haec generatio donec omnia haec fiant
Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
35 caelum et terra transibunt verba vero mea non praeteribunt
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
36 de die autem illa et hora nemo scit neque angeli caelorum nisi Pater solus
“Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
37 sicut autem in diebus Noe ita erit et adventus Filii hominis
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
38 sicut enim erant in diebus ante diluvium comedentes et bibentes nubentes et nuptum tradentes usque ad eum diem quo introivit in arcam Noe
Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
39 et non cognoverunt donec venit diluvium et tulit omnes ita erit et adventus Filii hominis
ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
40 tunc duo erunt in agro unus adsumetur et unus relinquetur
Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
41 duae molentes in mola una adsumetur et una relinquetur
Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
42 vigilate ergo quia nescitis qua hora Dominus vester venturus sit
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
43 illud autem scitote quoniam si sciret pater familias qua hora fur venturus esset vigilaret utique et non sineret perfodiri domum suam
Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
44 ideoque et vos estote parati quia qua nescitis hora Filius hominis venturus est
Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
45 quis putas est fidelis servus et prudens quem constituit dominus suus supra familiam suam ut det illis cibum in tempore
“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
46 beatus ille servus quem cum venerit dominus eius invenerit sic facientem
Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
47 amen dico vobis quoniam super omnia bona sua constituet eum
Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
48 si autem dixerit malus servus ille in corde suo moram facit dominus meus venire
Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
49 et coeperit percutere conservos suos manducet autem et bibat cum ebriis
Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
50 veniet dominus servi illius in die qua non sperat et hora qua ignorat
Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
51 et dividet eum partemque eius ponet cum hypocritis illic erit fletus et stridor dentium
Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.