< Mattheum 15 >
1 tunc accesserunt ad eum ab Hierosolymis scribae et Pharisaei dicentes
Sai wadansu Farisawa da malamai suka zo wurin Yesu daga Urushalima. Su ka ce,
2 quare discipuli tui transgrediuntur traditionem seniorum non enim lavant manus suas cum panem manducant
“Meyasa almajiranka suke karya al'adar dattawa? Don ba su wanke hannayen su kafin su ci abinci.”
3 ipse autem respondens ait illis quare et vos transgredimini mandatum Dei propter traditionem vestram
Yesu ya amsa masu ya ce, “Kuma don me ku ke karya dokar Allah saboda al'adunku?
4 nam Deus dixit honora patrem et matrem et qui maledixerit patri vel matri morte moriatur
Domin Allah ya ce, 'Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka; 'Shi wanda ya yi muguwar magana ga mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lallai zai mutu.
5 vos autem dicitis quicumque dixerit patri vel matri munus quodcumque est ex me tibi proderit
Amma kun ce, “Duk wanda ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, “Kowanne taimako da za ka samu daga gare ni yanzu baiko ne ga Allah,'”
6 et non honorificabit patrem suum aut matrem et irritum fecistis mandatum Dei propter traditionem vestram
wannan mutum ba ya bukatar ya girmama mahaifinsa. Ta wannan hanya kun maida maganar Allah wofi saboda al'adunku.
7 hypocritae bene prophetavit de vobis Esaias dicens
Ku munafukai, daidai ne Ishaya ya yi annabci akan ku da ya ce,
8 populus hic labiis me honorat cor autem eorum longe est a me
“Wadannan mutane girmama ni da baki kawai suke yi, amma zukatansu nesa suke da ni.
9 sine causa autem colunt me docentes doctrinas mandata hominum
Suna mani sujada a banza, domin suna koyar da dokokin mutane a matsayin rukunansu.”
10 et convocatis ad se turbis dixit eis audite et intellegite
Sai ya kira taron mutane zuwa gare shi ya ce masu, “Ku saurara ku fahimta,
11 non quod intrat in os coinquinat hominem sed quod procedit ex ore hoc coinquinat hominem
ba abin da ke shiga baki ke kazantar da mutum ba. Sai dai, abin da ke fitowa daga baki, wannan shi ya ke kazantar da mutum.”
12 tunc accedentes discipuli eius dixerunt ei scis quia Pharisaei audito verbo scandalizati sunt
Sai al'majiran suka zo suka ce masa, “Ka san Farisawa ba su ji dadi ba da suka ji maganan nan?”
13 at ille respondens ait omnis plantatio quam non plantavit Pater meus caelestis eradicabitur
Yesu ya amsa ya ce, “Kowace shuka wadda ba Ubana na sama ya shuka ba za a tuge ta.
14 sinite illos caeci sunt duces caecorum caecus autem si caeco ducatum praestet ambo in foveam cadunt
Ku kyale su kawai, su makafin jagora ne. In makaho ya ja wa wani makaho gora dukan su za su fada rami.”
15 respondens autem Petrus dixit ei edissere nobis parabolam istam
Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, “Ka bayyana wannan misali a garemu,”
16 at ille dixit adhuc et vos sine intellectu estis
Yesu ya ce, “Ku ma har yanzu ba ku da fahimta?
17 non intellegitis quia omne quod in os intrat in ventrem vadit et in secessum emittitur
Ko baku gani ba duk abin da ke shiga baki zuwa ciki ta haka yake fita zuwa salga?
18 quae autem procedunt de ore de corde exeunt et ea coinquinant hominem
Amma abubuwan da ke fita daga baki suna fitowa ne daga zuciya. Su ne abubuwan da ke kazantar da mutum.
19 de corde enim exeunt cogitationes malae homicidia adulteria fornicationes furta falsa testimonia blasphemiae
Domin daga zuciya mugayen tunani suke fitowa, kisan kai, zina, fasikanci, sata, shaidar zur, da zage-zage.
20 haec sunt quae coinquinant hominem non lotis autem manibus manducare non coinquinat hominem
Wadannan su ne abubuwan da ke kazantar da mutum. Amma ci da rashin wanke hannu baya kazantar da mutum.”
21 et egressus inde Iesus secessit in partes Tyri et Sidonis
Sai Yesu ya tafi daga nan ya nufi yankin biranen Taya da Sidon.
22 et ecce mulier chananea a finibus illis egressa clamavit dicens ei miserere mei Domine Fili David filia mea male a daemonio vexatur
Sai wata mace Bakan'aniya ta zo daga wannan yanki. Ta daga murya ta ce,” Ka yi mani jinkai, Ubangiji, Dan Dauda; 'yata tana cikin bakar azaba da aljani.”
23 qui non respondit ei verbum et accedentes discipuli eius rogabant eum dicentes dimitte eam quia clamat post nos
Amma Yesu bai ce mata kome ba. Almajiransa suka zo suka roke shi, suna cewa, “Ka sallame ta, domin tana bin mu da ihu.”
24 ipse autem respondens ait non sum missus nisi ad oves quae perierunt domus Israhel
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Ba a aike ni gun kowa ba sai dai ga batattun tumakin gidan Isra'ila.”
25 at illa venit et adoravit eum dicens Domine adiuva me
Amma ta zo ta durkusa a gabansa, tana cewa, “Ubangiji ka taimake ni.”
26 qui respondens ait non est bonum sumere panem filiorum et mittere canibus
Ya amsa ya ce, “Ba daidai bane a dauki gurasar yara a jefa wa kananan karnuka.
27 at illa dixit etiam Domine nam et catelli edunt de micis quae cadunt de mensa dominorum suorum
Ta ce, “I, Ubangiji, amma ko kananan karnuka suna cin barbashin da ke fadowa daga teburin maigida.”
28 tunc respondens Iesus ait illi o mulier magna est fides tua fiat tibi sicut vis et sanata est filia illius ex illa hora
Sai Yesu ya amsa ya ce mata, “Mace, bangaskiyarki tana da girma. Bari ya zamar maki yadda ki ke so.”'Yarta ta warke a lokacin.
29 et cum transisset inde Iesus venit secus mare Galilaeae et ascendens in montem sedebat ibi
Yesu ya bar wurin ya tafi kusa da tekun Galili. Sai ya hau tudu ya zauna a can.
30 et accesserunt ad eum turbae multae habentes secum mutos clodos caecos debiles et alios multos et proiecerunt eos ad pedes eius et curavit eos
Taro mai yawa suka zo gunsa. Suka kawo masa guragu, makafi, bebaye da nakasassun mutane da yawa, da wadansu marasa lafiya. Suka kawo su gaban Yesu, sai ya warkar da su.
31 ita ut turbae mirarentur videntes mutos loquentes clodos ambulantes caecos videntes et magnificabant Deum Israhel
Don haka mutane da yawa suka yi mamaki a lokacin da suka ga bebaye suna magana, nakasassu sun warke, guragu suna tafiya, makafi suna gani. Sai suka daukaka Allah na Isra'ila.
32 Iesus autem convocatis discipulis suis dixit misereor turbae quia triduo iam perseverant mecum et non habent quod manducent et dimittere eos ieiunos nolo ne deficiant in via
Yesu ya kira almajiransa zuwa gun sa sai ya ce, “Ina jin tausayin taron, sun kasance tare da ni kwana uku ke nan kuma ba su da abin da za su ci. Bana so in sallame su ba tare da sun ci abinci ba, domin kada su suma a hanya.”
33 et dicunt ei discipuli unde ergo nobis in deserto panes tantos ut saturemus turbam tantam
Almajiran suka ce masa, “A ina zamu sami isasshiyar gurasa a wannan wuri da babu kowa har ta ishi babban taron nan.”
34 et ait illis Iesus quot panes habetis at illi dixerunt septem et paucos pisciculos
Yesu ya ce masu, “Gurasa nawa ku ke da ita?” Suka ce, “Bakwai da 'yan kifi marasa yawa.”
35 et praecepit turbae ut discumberet super terram
Sai Yesu ya umarci taron su zauna a kasa.
36 et accipiens septem panes et pisces et gratias agens fregit et dedit discipulis suis et discipuli dederunt populo
Ya dauki gurasar nan bakwai da kifin, bayan ya yi godiya, ya kakkarya gurasar ya bada ita ga almajiran Sai almajiran suka ba taron.
37 et comederunt omnes et saturati sunt et quod superfuit de fragmentis tulerunt septem sportas plenas
Jama'a duka suka ci suka koshi. Suka tattara gutsattsarin abincin da ya rage, kwando bakwai cike.
38 erant autem qui manducaverant quattuor milia hominum extra parvulos et mulieres
Wadanda suka ci su dubu hudu ne maza, banda mata da yara.
39 et dimissa turba ascendit in naviculam et venit in fines Magedan
Sai Yesu ya sallami taron ya shiga cikin jirgin ruwa ya tafi yankin Magadan.