< Lucam 1 >

1 quoniam quidem multi conati sunt ordinare narrationem quae in nobis conpletae sunt rerum
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 sicut tradiderunt nobis qui ab initio ipsi viderunt et ministri fuerunt sermonis
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 visum est et mihi adsecuto a principio omnibus diligenter ex ordine tibi scribere optime Theophile
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 ut cognoscas eorum verborum de quibus eruditus es veritatem
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 fuit in diebus Herodis regis Iudaeae sacerdos quidam nomine Zaccharias de vice Abia et uxor illi de filiabus Aaron et nomen eius Elisabeth
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 erant autem iusti ambo ante Deum incedentes in omnibus mandatis et iustificationibus Domini sine querella
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 et non erat illis filius eo quod esset Elisabeth sterilis et ambo processissent in diebus suis
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 factum est autem cum sacerdotio fungeretur in ordine vicis suae ante Deum
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 secundum consuetudinem sacerdotii sorte exiit ut incensum poneret ingressus in templum Domini
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 et omnis multitudo erat populi orans foris hora incensi
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 apparuit autem illi angelus Domini stans a dextris altaris incensi
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 et Zaccharias turbatus est videns et timor inruit super eum
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 ait autem ad illum angelus ne timeas Zaccharia quoniam exaudita est deprecatio tua et uxor tua Elisabeth pariet tibi filium et vocabis nomen eius Iohannem
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 et erit gaudium tibi et exultatio et multi in nativitate eius gaudebunt
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 erit enim magnus coram Domino et vinum et sicera non bibet et Spiritu Sancto replebitur adhuc ex utero matris suae
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 et multos filiorum Israhel convertet ad Dominum Deum ipsorum
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 et ipse praecedet ante illum in spiritu et virtute Heliae ut convertat corda patrum in filios et incredibiles ad prudentiam iustorum parare Domino plebem perfectam
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 et dixit Zaccharias ad angelum unde hoc sciam ego enim sum senex et uxor mea processit in diebus suis
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 et respondens angelus dixit ei ego sum Gabrihel qui adsto ante Deum et missus sum loqui ad te et haec tibi evangelizare
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 et ecce eris tacens et non poteris loqui usque in diem quo haec fiant pro eo quod non credidisti verbis meis quae implebuntur in tempore suo
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 et erat plebs expectans Zacchariam et mirabantur quod tardaret ipse in templo
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 egressus autem non poterat loqui ad illos et cognoverunt quod visionem vidisset in templo et ipse erat innuens illis et permansit mutus
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 et factum est ut impleti sunt dies officii eius abiit in domum suam
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 post hos autem dies concepit Elisabeth uxor eius et occultabat se mensibus quinque dicens
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 quia sic mihi fecit Dominus in diebus quibus respexit auferre obprobrium meum inter homines
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 in mense autem sexto missus est angelus Gabrihel a Deo in civitatem Galilaeae cui nomen Nazareth
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 ad virginem desponsatam viro cui nomen erat Ioseph de domo David et nomen virginis Maria
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 et ingressus angelus ad eam dixit have gratia plena Dominus tecum benedicta tu in mulieribus
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 quae cum vidisset turbata est in sermone eius et cogitabat qualis esset ista salutatio
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 et ait angelus ei ne timeas Maria invenisti enim gratiam apud Deum
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 ecce concipies in utero et paries filium et vocabis nomen eius Iesum
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 hic erit magnus et Filius Altissimi vocabitur et dabit illi Dominus Deus sedem David patris eius
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 et regnabit in domo Iacob in aeternum et regni eius non erit finis (aiōn g165)
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
34 dixit autem Maria ad angelum quomodo fiet istud quoniam virum non cognosco
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 et respondens angelus dixit ei Spiritus Sanctus superveniet in te et virtus Altissimi obumbrabit tibi ideoque et quod nascetur sanctum vocabitur Filius Dei
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 et ecce Elisabeth cognata tua et ipsa concepit filium in senecta sua et hic mensis est sextus illi quae vocatur sterilis
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 quia non erit inpossibile apud Deum omne verbum
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 dixit autem Maria ecce ancilla Domini fiat mihi secundum verbum tuum et discessit ab illa angelus
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 exsurgens autem Maria in diebus illis abiit in montana cum festinatione in civitatem Iuda
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 et intravit in domum Zacchariae et salutavit Elisabeth
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 et factum est ut audivit salutationem Mariae Elisabeth exultavit infans in utero eius et repleta est Spiritu Sancto Elisabeth
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 et exclamavit voce magna et dixit benedicta tu inter mulieres et benedictus fructus ventris tui
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 et unde hoc mihi ut veniat mater Domini mei ad me
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 ecce enim ut facta est vox salutationis tuae in auribus meis exultavit in gaudio infans in utero meo
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 et beata quae credidit quoniam perficientur ea quae dicta sunt ei a Domino
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 et ait Maria magnificat anima mea Dominum
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 et exultavit spiritus meus in Deo salutari meo
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 quia respexit humilitatem ancillae suae ecce enim ex hoc beatam me dicent omnes generationes
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 quia fecit mihi magna qui potens est et sanctum nomen eius
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 et misericordia eius in progenies et progenies timentibus eum
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 fecit potentiam in brachio suo dispersit superbos mente cordis sui
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 deposuit potentes de sede et exaltavit humiles
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 esurientes implevit bonis et divites dimisit inanes
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 suscepit Israhel puerum suum memorari misericordiae
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 sicut locutus est ad patres nostros Abraham et semini eius in saecula (aiōn g165)
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
56 mansit autem Maria cum illa quasi mensibus tribus et reversa est in domum suam
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Elisabeth autem impletum est tempus pariendi et peperit filium
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 et audierunt vicini et cognati eius quia magnificavit Dominus misericordiam suam cum illa et congratulabantur ei
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 et factum est in die octavo venerunt circumcidere puerum et vocabant eum nomine patris eius Zacchariam
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 et respondens mater eius dixit nequaquam sed vocabitur Iohannes
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 et dixerunt ad illam quia nemo est in cognatione tua qui vocetur hoc nomine
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 innuebant autem patri eius quem vellet vocari eum
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 et postulans pugillarem scripsit dicens Iohannes est nomen eius et mirati sunt universi
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 apertum est autem ilico os eius et lingua eius et loquebatur benedicens Deum
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 et factus est timor super omnes vicinos eorum et super omnia montana Iudaeae divulgabantur omnia verba haec
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 et posuerunt omnes qui audierant in corde suo dicentes quid putas puer iste erit etenim manus Domini erat cum illo
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 et Zaccharias pater eius impletus est Spiritu Sancto et prophetavit dicens
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 benedictus Deus Israhel quia visitavit et fecit redemptionem plebi suae
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 et erexit cornu salutis nobis in domo David pueri sui
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 sicut locutus est per os sanctorum qui a saeculo sunt prophetarum eius (aiōn g165)
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
71 salutem ex inimicis nostris et de manu omnium qui oderunt nos
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 ad faciendam misericordiam cum patribus nostris et memorari testamenti sui sancti
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 iusiurandum quod iuravit ad Abraham patrem nostrum
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 daturum se nobis ut sine timore de manu inimicorum nostrorum liberati serviamus illi
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 in sanctitate et iustitia coram ipso omnibus diebus nostris
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 et tu puer propheta Altissimi vocaberis praeibis enim ante faciem Domini parare vias eius
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 ad dandam scientiam salutis plebi eius in remissionem peccatorum eorum
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 per viscera misericordiae Dei nostri in quibus visitavit nos oriens ex alto
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 inluminare his qui in tenebris et in umbra mortis sedent ad dirigendos pedes nostros in viam pacis
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 puer autem crescebat et confortabatur spiritu et erat in deserto usque in diem ostensionis suae ad Israhel
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.

< Lucam 1 >