< Lucam 17 >
1 et ad discipulos suos ait inpossibile est ut non veniant scandala vae autem illi per quem veniunt
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 utilius est illi si lapis molaris inponatur circa collum eius et proiciatur in mare quam ut scandalizet unum de pusillis istis
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 adtendite vobis si peccaverit frater tuus increpa illum et si paenitentiam egerit dimitte illi
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 et si septies in die peccaverit in te et septies in die conversus fuerit ad te dicens paenitet me dimitte illi
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 et dixerunt apostoli Domino adauge nobis fidem
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 dixit autem Dominus si haberetis fidem sicut granum sinapis diceretis huic arbori moro eradicare et transplantare in mare et oboediret vobis
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 quis autem vestrum habens servum arantem aut pascentem qui regresso de agro dicet illi statim transi recumbe
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 et non dicet ei para quod cenem et praecinge te et ministra mihi donec manducem et bibam et post haec tu manducabis et bibes
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 numquid gratiam habet servo illi quia fecit quae sibi imperaverat non puto
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 sic et vos cum feceritis omnia quae praecepta sunt vobis dicite servi inutiles sumus quod debuimus facere fecimus
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 et factum est dum iret in Hierusalem transiebat per mediam Samariam et Galilaeam
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 et cum ingrederetur quoddam castellum occurrerunt ei decem viri leprosi qui steterunt a longe
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 et levaverunt vocem dicentes Iesu praeceptor miserere nostri
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 quos ut vidit dixit ite ostendite vos sacerdotibus et factum est dum irent mundati sunt
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 unus autem ex illis ut vidit quia mundatus est regressus est cum magna voce magnificans Deum
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 et cecidit in faciem ante pedes eius gratias agens et hic erat Samaritanus
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 respondens autem Iesus dixit nonne decem mundati sunt et novem ubi sunt
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 non est inventus qui rediret et daret gloriam Deo nisi hic alienigena
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 et ait illi surge vade quia fides tua te salvum fecit
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 interrogatus autem a Pharisaeis quando venit regnum Dei respondit eis et dixit non venit regnum Dei cum observatione
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 neque dicent ecce hic aut ecce illic ecce enim regnum Dei intra vos est
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 et ait ad discipulos venient dies quando desideretis videre unum diem Filii hominis et non videbitis
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 et dicent vobis ecce hic ecce illic nolite ire neque sectemini
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 nam sicut fulgur coruscans de sub caelo in ea quae sub caelo sunt fulget ita erit Filius hominis in die sua
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 primum autem oportet illum multa pati et reprobari a generatione hac
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 et sicut factum est in diebus Noe ita erit et in diebus Filii hominis
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 edebant et bibebant uxores ducebant et dabantur ad nuptias usque in diem qua intravit Noe in arcam et venit diluvium et perdidit omnes
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 similiter sicut factum est in diebus Loth edebant et bibebant emebant et vendebant plantabant aedificabant
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 qua die autem exiit Loth a Sodomis pluit ignem et sulphur de caelo et omnes perdidit
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 secundum haec erit qua die Filius hominis revelabitur
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 in illa hora qui fuerit in tecto et vasa eius in domo ne descendat tollere illa et qui in agro similiter non redeat retro
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 memores estote uxoris Loth
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 quicumque quaesierit animam suam salvare perdet illam et qui perdiderit illam vivificabit eam
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 dico vobis illa nocte erunt duo in lecto uno unus adsumetur et alter relinquetur
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 duae erunt molentes in unum una adsumetur et altera relinquetur duo in agro unus adsumetur et alter relinquetur
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
36 respondentes dicunt illi ubi Domine
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 qui dixit eis ubicumque fuerit corpus illuc congregabuntur aquilae
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”