< Lamentationes 3 >

1 ALEPH ego vir videns paupertatem meam in virga indignationis eius
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 ALEPH me minavit et adduxit in tenebris et non in lucem
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 ALEPH tantum in me vertit et convertit manum suam tota die
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 BETH vetustam fecit pellem meam et carnem meam contrivit ossa mea
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 BETH aedificavit in gyro meo et circumdedit me felle et labore
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 BETH in tenebrosis conlocavit me quasi mortuos sempiternos
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 GIMEL circumaedificavit adversum me ut non egrediar adgravavit conpedem meam
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 GIMEL sed et cum clamavero et rogavero exclusit orationem meam
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 GIMEL conclusit vias meas lapidibus quadris semitas meas subvertit
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 DELETH ursus insidians factus est mihi leo in absconditis
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 DELETH semitas meas subvertit et confregit me posuit me desolatam
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 DELETH tetendit arcum suum et posuit me quasi signum ad sagittam
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 HE misit in renibus meis filias faretrae suae
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 HE factus sum in derisu omni populo meo canticum eorum tota die
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 HE replevit me amaritudinibus inebriavit me absinthio
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 VAV et fregit ad numerum dentes meos cibavit me cinere
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 VAV et repulsa est anima mea oblitus sum bonorum
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 VAV et dixi periit finis meus et spes mea a Domino
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 ZAI recordare paupertatis et transgressionis meae absinthii et fellis
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 ZAI memoria memor ero et tabescet in me anima mea
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 ZAI hoc recolens in corde meo ideo sperabo
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 HETH misericordiae Domini quia non sumus consumpti quia non defecerunt miserationes eius
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 HETH novae diluculo multa est fides tua
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 HETH pars mea Dominus dixit anima mea propterea expectabo eum
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 TETH bonus est Dominus sperantibus in eum animae quaerenti illum
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 TETH bonum est praestolari cum silentio salutare Domini
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 TETH bonum est viro cum portaverit iugum ab adulescentia sua
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 IOTH sedebit solitarius et tacebit quia levavit super se
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 IOTH ponet in pulvere os suum si forte sit spes
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 IOTH dabit percutienti se maxillam saturabitur obprobriis
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 CAPH quia non repellet in sempiternum Dominus
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 CAPH quia si abiecit et miserebitur secundum multitudinem misericordiarum suarum
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 CAPH non enim humiliavit ex corde suo et abiecit filios hominis
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 LAMED ut contereret sub pedibus suis omnes vinctos terrae
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 LAMED ut declinaret iudicium viri in conspectu vultus Altissimi
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 LAMED ut perverteret hominem in iudicio suo Dominus ignoravit
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 MEM quis est iste qui dixit ut fieret Domino non iubente
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 MEM ex ore Altissimi non egredientur nec mala nec bona
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 MEM quid murmuravit homo vivens vir pro peccatis suis
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 NUN scrutemur vias nostras et quaeramus et revertamur ad Dominum
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 NUN levemus corda nostra cum manibus ad Dominum in caelos
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 NUN nos inique egimus et ad iracundiam provocavimus idcirco tu inexorabilis es
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 SAMECH operuisti in furore et percussisti nos occidisti nec pepercisti
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 SAMECH opposuisti nubem tibi ne transeat oratio
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 SAMECH eradicationem et abiectionem posuisti me in medio populorum
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 FE aperuerunt super nos os suum omnes inimici
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 FE formido et laqueus facta est nobis vaticinatio et contritio
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 FE divisiones aquarum deduxit oculus meus in contritione filiae populi mei
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 AIN oculus meus adflictus est nec tacuit eo quod non esset requies
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 AIN donec respiceret et videret Dominus de caelis
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 AIN oculus meus depraedatus est animam meam in cunctis filiabus urbis meae
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 SADE venatione ceperunt me quasi avem inimici mei gratis
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 SADE lapsa est in lacu vita mea et posuerunt lapidem super me
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 SADE inundaverunt aquae super caput meum dixi perii
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 COPH invocavi nomen tuum Domine de lacis novissimis
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 COPH vocem meam audisti ne avertas aurem tuam a singultu meo et clamoribus
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 COPH adpropinquasti in die quando invocavi te dixisti ne timeas
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 RES iudicasti Domine causam animae meae redemptor vitae meae
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 RES vidisti Domine iniquitatem adversum me iudica iudicium meum
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 RES vidisti omnem furorem universas cogitationes eorum adversum me
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 SEN audisti obprobria eorum Domine omnes cogitationes eorum adversum me
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 SEN labia insurgentium mihi et meditationes eorum adversum me tota die
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 SEN sessionem eorum et resurrectionem eorum vide ego sum psalmus eorum
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 THAU reddes eis vicem Domine iuxta opera manuum suarum
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 THAU dabis eis scutum cordis laborem tuum
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 THAU persequeris in furore et conteres eos sub caelis Domine
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentationes 3 >