< Job 4 >

1 respondens autem Eliphaz Themanites dixit
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 si coeperimus loqui tibi forsitan moleste accipias sed conceptum sermonem tenere quis possit
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 ecce docuisti multos et manus lassas roborasti
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 vacillantes confirmaverunt sermones tui et genua trementia confortasti
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 nunc autem venit super te plaga et defecisti tetigit te et conturbatus es
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 timor tuus fortitudo tua patientia tua et perfectio viarum tuarum
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 recordare obsecro te quis umquam innocens perierit aut quando recti deleti sint
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 quin potius vidi eos qui operantur iniquitatem et seminant dolores et metunt eos
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 flante Deo perisse et spiritu irae eius esse consumptos
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 rugitus leonis et vox leaenae et dentes catulorum leonum contriti sunt
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 tigris periit eo quod non haberet praedam et catuli leonis dissipati sunt
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 porro ad me dictum est verbum absconditum et quasi furtive suscepit auris mea venas susurri eius
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 in horrore visionis nocturnae quando solet sopor occupare homines
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 pavor tenuit me et tremor et omnia ossa mea perterrita sunt
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 et cum spiritus me praesente transiret inhorruerunt pili carnis meae
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 stetit quidam cuius non agnoscebam vultum imago coram oculis meis et vocem quasi aurae lenis audivi
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 numquid homo Dei conparatione iustificabitur aut factore suo purior erit vir
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 ecce qui serviunt ei non sunt stabiles et in angelis suis repperit pravitatem
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 quanto magis hii qui habitant domos luteas qui terrenum habent fundamentum consumentur velut a tinea
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 de mane usque ad vesperum succidentur et quia nullus intellegit in aeternum peribunt
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 qui autem reliqui fuerint auferentur ex eis morientur et non in sapientia
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

< Job 4 >