< Job 34 >

1 pronuntians itaque Heliu etiam haec locutus est
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 audite sapientes verba mea et eruditi auscultate me
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 auris enim verba probat et guttur escas gustu diiudicat
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 iudicium eligamus nobis et inter nos videamus quid sit melius
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 quia dixit Iob iustus sum et Deus subvertit iudicium meum
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 in iudicando enim me mendacium est violenta sagitta mea absque ullo peccato
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 quis est vir ut est Iob qui bibit subsannationem quasi aquam
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 qui graditur cum operantibus iniquitatem et ambulat cum viris impiis
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 dixit enim non placebit vir Deo etiam si cucurrerit cum eo
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 ideo viri cordati audite me absit a Deo impietas et ab Omnipotente iniquitas
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 opus enim hominis reddet ei et iuxta vias singulorum restituet
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 vere enim Deus non condemnabit frustra nec Omnipotens subvertet iudicium
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 quem constituit alium super terram aut quem posuit super orbem quem fabricatus est
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 si direxerit ad eum cor suum spiritum illius et flatum ad se trahet
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 deficiet omnis caro simul et homo in cinerem revertetur
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 si habes ergo intellectum audi quod dicitur et ausculta vocem eloquii mei
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 numquid qui non amat iudicium sanare potest et quomodo tu eum qui iustus est in tantum condemnas
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 qui dicit regi apostata qui vocat duces impios
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 qui non accipit personas principum nec cognovit tyrannum cum disceptaret contra pauperem opus enim manuum eius sunt universi
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 subito morientur et in media nocte turbabuntur populi et pertransibunt et auferent violentum absque manu
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 oculi enim eius super vias hominum et omnes gressus eorum considerat
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 non sunt tenebrae et non est umbra mortis ut abscondantur ibi qui operantur iniquitatem
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 neque enim ultra in hominis potestate est ut veniat ad Deum in iudicium
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 conteret multos innumerabiles et stare faciet alios pro eis
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 novit enim opera eorum et idcirco inducet noctem et conterentur
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 quasi impios percussit eos in loco videntium
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 qui quasi de industria recesserunt ab eo et omnes vias eius intellegere noluerunt
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 ut pervenire facerent ad eum clamorem egeni et audiret vocem pauperum
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 ipso enim concedente pacem quis est qui condemnet ex quo absconderit vultum quis est qui contempletur eum et super gentem et super omnes homines
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 qui regnare facit hominem hypocritam propter peccata populi
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 quia ergo ego locutus sum ad Deum te quoque non prohibeo
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 si erravi tu doce me si iniquitatem locutus sum ultra non addam
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 numquid a te Deus expetit eam quia displicuit tibi tu enim coepisti loqui et non ego quod si quid nosti melius loquere
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 viri intellegentes loquantur mihi et vir sapiens audiat me
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Iob autem stulte locutus est et verba illius non sonant disciplinam
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 pater mi probetur Iob usque ad finem ne desinas in hominibus iniquitatis
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 quia addit super peccata sua blasphemiam inter nos interim constringatur et tunc ad iudicium provocet sermonibus suis Deum
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >