< Job 33 >
1 audi igitur Iob eloquia mea et omnes sermones meos ausculta
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 ecce aperui os meum loquatur lingua mea in faucibus meis
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 simplici corde meo sermones mei et sententiam labia mea puram loquentur
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 spiritus Dei fecit me et spiraculum Omnipotentis vivificavit me
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 si potes responde mihi et adversus faciem meam consiste
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 ecce et me sicut et te fecit Deus et de eodem luto ego quoque formatus sum
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 verumtamen miraculum meum non te terreat et eloquentia mea non sit tibi gravis
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 dixisti ergo in auribus meis et vocem verborum audivi
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 mundus sum ego absque delicto inmaculatus et non est iniquitas in me
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 quia querellas in me repperit ideo arbitratus est me inimicum sibi
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 posuit in nervo pedes meos custodivit omnes semitas meas
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 hoc est ergo in quo non es iustificatus respondebo tibi quia maior sit Deus homine
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 adversum eum contendis quod non ad omnia verba responderit tibi
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 semel loquitur Deus et secundo id ipsum non repetit
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 per somnium in visione nocturna quando inruit sopor super homines et dormiunt in lectulo
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 tunc aperit aures virorum et erudiens eos instruit disciplinam
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 ut avertat hominem ab his quae facit et liberet eum de superbia
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 eruens animam eius a corruptione et vitam illius ut non transeat in gladium
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 increpat quoque per dolorem in lectulo et omnia ossa eius marcescere facit
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 abominabilis ei fit in vita sua panis et animae illius cibus ante desiderabilis
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 tabescet caro eius et ossa quae tecta fuerant nudabuntur
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 adpropinquabit corruptioni anima eius et vita illius mortiferis
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 si fuerit pro eo angelus loquens unum de milibus ut adnuntiet hominis aequitatem
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 miserebitur eius et dicet libera eum et non descendat in corruptionem inveni in quo ei propitier
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 consumpta est caro eius a suppliciis revertatur ad dies adulescentiae suae
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 deprecabitur Deum et placabilis ei erit et videbit faciem eius in iubilo et reddet homini iustitiam suam
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 respiciet homines et dicet peccavi et vere deliqui et ut eram dignus non recepi
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 liberavit animam suam ne pergeret in interitum sed vivens lucem videret
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 ecce haec omnia operatur Deus tribus vicibus per singulos
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 ut revocet animas eorum a corruptione et inluminet luce viventium
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 adtende Iob et audi me et tace dum ego loquar
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 si autem habes quod loquaris responde mihi loquere volo enim te apparere iustum
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 quod si non habes audi me tace et docebo te sapientiam
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”