< Job 32 >

1 omiserunt autem tres viri isti respondere Iob eo quod iustus sibi videretur
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 et iratus indignatusque Heliu filius Barachel Buzites de cognatione Ram iratus est autem adversus Iob eo quod iustum se esse diceret coram Deo
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 porro adversum amicos eius indignatus est eo quod non invenissent responsionem rationabilem sed tantummodo condemnassent Iob
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 igitur Heliu expectavit Iob loquentem eo quod seniores se essent qui loquebantur
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 cum autem vidisset quod tres respondere non potuissent iratus est vehementer
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 respondensque Heliu filius Barachel Buzites dixit iunior sum tempore vos autem antiquiores idcirco dimisso capite veritus sum indicare vobis meam sententiam
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 sperabam enim quod aetas prolixior loqueretur et annorum multitudo doceret sapientiam
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 sed ut video spiritus est in hominibus et inspiratio Omnipotentis dat intellegentiam
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 non sunt longevi sapientes nec senes intellegunt iudicium
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 ideo dicam audite me ostendam vobis etiam ego meam scientiam
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 expectavi enim sermones vestros audivi prudentiam vestram donec disceptaremini sermonibus
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 et donec putabam vos aliquid dicere considerabam sed ut video non est qui arguere possit Iob et respondere ex vobis sermonibus eius
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 ne forte dicatis invenimus sapientiam Deus proiecit eum non homo
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 nihil locutus est mihi et ego non secundum vestros sermones respondebo illi
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 extimuerunt non responderunt ultra abstuleruntque a se eloquia
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 quoniam igitur expectavi et non sunt locuti steterunt nec responderunt ultra
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 respondebo et ego partem meam et ostendam scientiam meam
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 plenus sum enim sermonibus et coartat me spiritus uteri mei
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 en venter meus quasi mustum absque spiraculo quod lagunculas novas disrumpit
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 loquar et respirabo paululum aperiam labia mea et respondebo
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 non accipiam personam viri et Deum homini non aequabo
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 nescio enim quamdiu subsistam et si post modicum tollat me factor meus
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.

< Job 32 >