< Job 31 >
1 pepigi foedus cum oculis meis ut ne cogitarem quidem de virgine
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 quam enim partem haberet Deus in me desuper et hereditatem Omnipotens de excelsis
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 numquid non perditio est iniquo et alienatio operantibus iniustitiam
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 nonne ipse considerat vias meas et cunctos gressus meos dinumerat
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 si ambulavi in vanitate et festinavit in dolo pes meus
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 adpendat me in statera iusta et sciat Deus simplicitatem meam
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 si declinavit gressus meus de via et si secutum est oculos meos cor meum et in manibus meis adhesit macula
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 seram et alius comedat et progenies mea eradicetur
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 si deceptum est cor meum super mulierem et si ad ostium amici mei insidiatus sum
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 scortum sit alteri uxor mea et super illam incurventur alii
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 hoc enim nefas est et iniquitas maxima
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 ignis est usque ad perditionem devorans et omnia eradicans genimina
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 si contempsi subire iudicium cum servo meo et ancillae meae cum disceptarent adversum me
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 quid enim faciam cum surrexerit ad iudicandum Deus et cum quaesierit quid respondebo illi
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 numquid non in utero fecit me qui et illum operatus est et formavit in vulva unus
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 si negavi quod volebant pauperibus et oculos viduae expectare feci
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 si comedi buccellam meam solus et non comedit pupillus ex ea
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 quia ab infantia mea crevit mecum miseratio et de utero matris meae egressa est mecum
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 si despexi pereuntem eo quod non habuerit indumentum et absque operimento pauperem
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 si non benedixerunt mihi latera eius et de velleribus ovium mearum calefactus est
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 si levavi super pupillum manum meam etiam cum viderem me in porta superiorem
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 umerus meus a iunctura sua cadat et brachium meum cum suis ossibus confringatur
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 semper enim quasi tumentes super me fluctus timui Deum et pondus eius ferre non potui
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 si putavi aurum robur meum et obrizae dixi fiducia mea
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 si laetatus sum super multis divitiis meis et quia plurima repperit manus mea
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 si vidi solem cum fulgeret et lunam incedentem clare
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 et lactatum est in abscondito cor meum et osculatus sum manum meam ore meo
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 quae est iniquitas maxima et negatio contra Deum altissimum
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 si gavisus sum ad ruinam eius qui me oderat et exultavi quod invenisset eum malum
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 non enim dedi ad peccandum guttur meum ut expeterem maledicens animam eius
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 si non dixerunt viri tabernaculi mei quis det de carnibus eius ut saturemur
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 foris non mansit peregrinus ostium meum viatori patuit
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 si abscondi quasi homo peccatum meum et celavi in sinu meo iniquitatem meam
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 si expavi ad multitudinem nimiam et despectio propinquorum terruit me et non magis tacui nec egressus sum ostium
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 quis mihi tribuat auditorem ut desiderium meum Omnipotens audiat et librum scribat ipse qui iudicat
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 ut in umero meo portem illum et circumdem illum quasi coronam mihi
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 per singulos gradus meos pronuntiabo illum et quasi principi offeram eum
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 si adversum me terra mea clamat et cum ipsa sulci eius deflent
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 si fructus eius comedi absque pecunia et animam agricolarum eius adflixi
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 pro frumento oriatur mihi tribulus et pro hordeo spina finita sunt verba Iob
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.