< Job 25 >

1 respondens autem Baldad Suites dixit
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 potestas et terror apud eum est qui facit concordiam in sublimibus suis
“Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
3 numquid est numerus militum eius et super quem non surget lumen illius
Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
4 numquid iustificari potest homo conparatus Deo aut apparere mundus natus de muliere
Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
5 ecce etiam luna non splendet et stellae non sunt mundae in conspectu eius
In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
6 quanto magis homo putredo et filius hominis vermis
mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”

< Job 25 >